< Psalm 137 >

1 An Babels Strömen, da saßen wir und weinten, wenn Zions wir gedachten;
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 an die Weiden, die dort stehen, hängten wir unsre Harfen;
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 denn Lieder verlangten von uns dort unsre Zwingherrn, und unsre Peiniger hießen uns fröhlich sein: »Singt uns eins von euren Zionsliedern!«
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Wie sollten wir singen die Lieder des HERRN auf fremdem Boden?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Vergesse ich dich, Jerusalem, so verdorre mir die rechte Hand!
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Die Zunge bleibe mir am Gaumen kleben, wenn ich deiner nicht eingedenk bleibe, wenn ich Jerusalem nicht stelle über alles, was mir Freude macht!
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Gedenke, HERR, den Söhnen Edoms den Unglückstag Jerusalems, wie sie riefen: »Reißt nieder, reißt nieder bis auf den Grund in ihm!«
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Bewohnerschaft Babels, Verwüsterin! Heil dem, der dir vergilt dasselbe, was du an uns verübt!
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Heil dem, der deine Kindlein packt und am Felsen sie zerschmettert!
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalm 137 >