< Psalm 130 >

1 Ein Wallfahrtslied. Aus der Tiefe rufe ich, HERR, zu dir:
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 »Allherr, höre auf meine Stimme,
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Wenn du, HERR, Sünden behalten willst, o Allherr, wer kann bestehn!
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Doch bei dir ist die Vergebung, auf daß man dich fürchte.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 Ich harre des HERRN, meine Seele harrt, und ich warte auf sein Wort;
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 meine Seele harrt auf den Allherrn sehnsuchtsvoller als Wächter auf den Morgen.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Sehnsuchtsvoller als Wächter auf den Morgen harre, Israel, auf den HERRN! Denn beim HERRN ist die Gnade und Erlösung bei ihm in Fülle,
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 und er wird Israel erlösen von allen seinen Sünden.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalm 130 >