< Psalm 109 >
1 Dem Musikmeister; von David ein Psalm. Du Gott, dem mein Lobpreis gilt, bleibe nicht stumm!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Denn Frevlermund und Lügenmaul
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 mit Worten des Hasses haben sie mich umschwirrt und ohne Ursach’ mich angegriffen;
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 für meine Liebe befeinden sie mich, während ich doch (stets für sie) bete;
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 ja sie haben mir Böses für Gutes vergolten und Haß für meine Liebe erwiesen.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Bestell’ einen Frevler zum Richter gegen ihn, und ein Ankläger steh’ ihm zur Rechten!
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Als schuldig soll er hervorgehn aus dem Gericht und sogar sein Gebet ihm als Sünde gelten!
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Seiner Lebenstage müssen nur wenige sein, und sein Amt ein andrer empfangen!
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Seine Kinder müssen zu Waisen werden und seine Frau eine Witwe!
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Seine Kinder müssen unstet umherziehn und betteln und vertrieben werden aus ihres Vaterhauses Trümmern!
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Sein Gläubiger lege Beschlag auf alles, was er hat, und Fremde müssen seine Habe plündern!
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Er finde keinen, der ihm Schonung gewährt, und niemand habe Erbarmen mit seinen Waisen!
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Sein Nachwuchs müsse der Ausrottung verfallen: schon im zweiten Gliede müsse ihr Name erlöschen!
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Der Verschuldung seiner Väter werde beim HERRN gedacht, und die Sünde seiner Mutter bleibe ungetilgt!
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Sie müssen beständig dem HERRN vor Augen stehn, und er tilge ihr Gedächtnis aus von der Erde,
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 dieweil er nicht daran dachte, Liebe zu üben, vielmehr den Elenden und Armen verfolgte und den hoffnungslos Verzagten, ihn vollends zu töten.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Er liebte den Fluch: so treffe er ihn! Er hatte am Segen keine Freude: so bleib’ er ihm fern!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Er zog den Fluch an wie sein Kleid: so dringe er ihm in den Leib wie Wasser und wie Öl in seine Gebeine;
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 er werde ihm wie der Mantel, in den er sich hüllt, wie der Gürtel, den er sich ständig umlegt!
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Dies sei meiner Widersacher Lohn von seiten des HERRN und derer, die Böses gegen mich reden!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Du aber, HERR, mein Gott, tritt für mich ein um deines Namens willen! Weil deine Gnade köstlich ist, errette mich!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Denn elend bin ich und arm, und mein Herz ist verwundet in meiner Brust.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Wie ein Schatten, wenn er sich dehnt, so schwinde ich hin, bin vom Sturm verweht einer Heuschrecke gleich;
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 meine Knie wanken vom Fasten, mein Leib ist abgemagert, ohne Fett;
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 und ich – den Leuten bin ich zum Hohn geworden: sehen sie mich, so schütteln sie höhnend den Kopf.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Stehe mir bei, o HERR, mein Gott, hilf mir nach deiner Gnade!
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Laß sie erkennen, daß dies deine Hand ist, daß du, HERR, selbst es so gefügt hast!
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Sie mögen fluchen, du aber wollest segnen; erheben sie sich, so laß sie zuschanden werden, dein Knecht aber müsse sich freuen!
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Laß meine Widersacher in Schmach sich kleiden und ihre Schande umtun wie einen Mantel!
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Laut soll mein Mund dem HERRN Dank sagen, und inmitten vieler will ich ihn preisen;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 denn er steht dem Armen zur Rechten, um ihn zu retten vor denen, die ihn schuldig sprechen.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.