< Psalm 105 >

1 Preiset den HERRN, ruft seinen Namen an, macht seine Taten unter den Völkern bekannt!
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Singt ihm, spielet ihm, redet von all seinen Wundern!
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Rühmt euch seines heiligen Namens! Es mögen herzlich sich freun, die da suchen den HERRN!
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Fragt nach dem HERRN und seiner Stärke, suchet sein Angesicht allezeit!
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Gedenkt seiner Wunder, die er getan, seiner Zeichen und der Urteilssprüche seines Mundes,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 ihr Kinder Abrahams, seines Knechtes, ihr Söhne Jakobs, seine Erwählten!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Er, der HERR, ist unser Gott, über die ganze Erde ergehen seine Gerichte.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Er gedenkt seines Bundes auf ewig, des Wortes, das er geboten auf tausend Geschlechter,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 (des Bundes) den er mit Abraham geschlossen, und des Eides, den er Isaak geschworen,
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 den für Jakob er als Satzung bestätigt und für Israel als ewigen Bund,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 da er sprach: »Dir will ich Kanaan geben, das Land, das ich euch als Erbbesitztum zugeteilt!«
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Damals waren sie noch ein kleines Häuflein, gar wenige und nur Gäste im Lande;
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 sie mußten wandern von Volk zu Volk, von einem Reich zur andern Völkerschaft;
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 doch keinem gestattete er, sie zu bedrücken, ja Könige strafte er ihretwillen:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 »Tastet meine Gesalbten nicht an und tut meinen Propheten nichts zuleide!«
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Dann, als er Hunger ins Land ließ kommen und jegliche Stütze des Brotes zerbrach,
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 da hatte er schon einen Mann vor ihnen her gesandt: Joseph, der als Sklave verkauft war.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Man hatte seine Füße gezwängt in den Stock, in Eisen(-fesseln) war er gelegt,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 bis zu der Zeit, wo seine Weissagung eintraf und der Ausspruch des HERRN ihn als echt erwies.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Da sandte der König und ließ ihn entfesseln, der Völkergebieter, und machte ihn frei;
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 er bestellte ihn über sein Haus zum Herrn, zum Gebieter über sein ganzes Besitztum;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 er sollte über seine Fürsten schalten nach Belieben und seine höchsten Beamten Weisheit lehren.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 So kam denn Israel nach Ägypten, und Jakob weilte als Gast im Lande Hams.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Da machte Gott sein Volk gar fruchtbar und ließ es stärker werden als seine Bedränger;
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 er wandelte ihren Sinn, sein Volk zu hassen und Arglist an seinen Knechten zu üben.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Dann sandte er Mose, seinen Knecht, und Aaron, den er erkoren;
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 die richteten seine Zeichen unter ihnen aus und die Wunder im Lande Hams:
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Er sandte Finsternis und ließ es dunkel werden; doch sie achteten nicht auf seine Worte;
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 er verwandelte ihre Gewässer in Blut und ließ ihre Fische sterben;
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 es wimmelte ihr Land von Fröschen bis hinein in ihre Königsgemächer;
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 er gebot, da kamen Bremsenschwärme, Stechfliegen über ihr ganzes Gebiet;
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 er gab ihnen Hagelschauer als Regen, sandte flammendes Feuer in ihr Land;
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 er schlug ihre Reben und Feigenbäume und zerbrach die Bäume in ihrem Gebiet;
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 er gebot, da kamen die Heuschrecken und die Grillen in zahlloser Menge,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 die verzehrten alle Gewächse im Land und fraßen die Früchte ihrer Felder.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Dann schlug er alle Erstgeburt im Lande, die Erstlinge all ihrer Manneskraft.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Nun ließ er sie ausziehn mit Silber und Gold, und kein Strauchelnder war in seinen Stämmen;
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Ägypten war ihres Auszugs froh, denn Angst vor ihnen hatte sie befallen.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Er breitete Gewölk aus als Decke und Feuer, um ihnen die Nacht zu erhellen;
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 auf Moses Bitte ließ er Wachteln kommen und sättigte sie mit Himmelsbrot;
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 er spaltete einen Felsen: da rannen Wasser und flossen durch die Steppen als Strom;
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 denn er gedachte seines heiligen Wortes, dachte an Abraham, seinen Knecht.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 So ließ er sein Volk in Freuden ausziehn, unter Jubel seine Erwählten;
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 dann gab er ihnen die Länder der Heiden, und was die Völker erworben, das nahmen sie in Besitz,
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 auf daß sie seine Gebote halten möchten und seine Gesetze bewahrten. Halleluja!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalm 105 >