< Sprueche 4 >

1 Hört, ihr Kinder, die väterliche Unterweisung und merkt wohl auf, um Einsicht zu lernen!
Ku saurara’ya’yana ga koyarwar mahaifinku; ku mai da hankali, ku sami fahimi.
2 Denn treffliche Lehre gebe ich euch: laßt meine Weisungen nicht unbeachtet!
Ina ba ku sahihiyar koyarwa, saboda haka kada ku ƙyale koyarwata.
3 Denn als ich noch als Sohn bei meinem Vater war, als zartes und einziges Kind unter der Obhut meiner Mutter,
Sa’ad da nake yaro a gidan mahaifina, yaro kaɗai kuma na mahaifiyata,
4 da belehrte er mich und sagte zu mir: »Laß dein Herz meine Worte festhalten! Beobachte meine Weisungen, so wirst du leben.
ya koya mini ya ce, “Ka riƙe kalmomina da dukan zuciyarka; ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu.
5 Erwirb dir Weisheit, erwirb dir Einsicht, vergiß sie nicht und weiche nicht ab von den Worten meines Mundes!
Ka nemi hikima, ka nemi fahimi; kada ka manta da kalmomina ko ka kauce daga gare su.
6 Laß sie nicht außer acht, so wird sie dich behüten; gewinne sie lieb, so wird sie dich beschirmen.
Kada ka ƙyale hikima, za tă kuwa tsare ka; ka ƙaunace ta, za tă kuwa lura da kai.
7 Mit dem besten Teil deiner Habe erwirb dir Weisheit, und um den Preis deines ganzen Vermögens verschaffe dir Einsicht!
Hikima ce mafi girma duka; saboda haka ka nemi hikima. Ko da za tă ci duk abin da kake da shi, ka dai nemi fahimi.
8 Halte sie hoch, so wird sie dir Ansehen verleihen, wird dich zu Ehren bringen, wenn du sie mit Liebe umfängst;
Ka ƙaunace ta, za tă ɗaukaka ka; ka rungume ta, za tă kuwa girmama ka.
9 sie wird dir einen schönen Kranz aufs Haupt setzen, eine herrliche Krone dir bescheren.«
Za tă zama kayan ado da za su inganta kanka tă kuma zamar maka rawanin ɗaukaka.”
10 Höre, mein Sohn, und nimm meine Worte an, so werden dir viele Lebensjahre zuteil werden.
Ka saurara, ɗana, ka yarda da abin da na faɗa, shekarun rayuwarka kuwa za su zama masu yawa.
11 Über den Weg der Weisheit will ich dich belehren, will dich auf rechten Bahnen einhergehen lassen;
Na bishe ka a hanyar hikima na kuma jagorance ka a miƙaƙƙun hanyoyi.
12 wenn du (auf ihnen) wandelst, wird dein Schritt nicht gehemmt sein, und wenn du läufst, wirst du nicht zu Fall kommen.
Sa’ad da kake tafiya, ba abin da zai sa ka tuntuɓe; sa’ad da kake gudu, ba za ka fāɗi ba.
13 Halte an der Zucht fest, laß sie nicht fahren! Bewahre sie, denn sie ist dein Leben.
Ka riƙe umarni, kada ka bari yă kuɓuce; ka tsare shi sosai, gama ranka ne.
14 Begib dich nicht auf den Pfad der Gottlosen und schreite nicht einher auf dem Wege der Bösen!
Kada ka sa ƙafa a kan hanyar mugaye kada ka bi gurbin mugaye.
15 Meide ihn, gehe nicht auf ihn hinüber! Wende dich von ihm ab und gehe daran vorüber!
Ka guji mugunta, kada ka yi tafiya a kanta; juya daga gare ta ka yi tafiyarka.
16 Denn sie können nicht schlafen, wenn sie nicht Böses (zuvor) getan haben; und der Schlaf ist ihnen geraubt, wenn sie nicht jemand verführt haben;
Mugaye ba sa iya barci, sai sun aikata mugunta; ba su barci sai sun cuci wani.
17 denn das Brot, das sie essen, ist Gottlosigkeit, und der Wein, den sie trinken, ist Gewalttätigkeit.
Mugunta da ta’adi kamar ci da sha suke a gare su.
18 Aber der Pfad der Gerechten gleicht dem Glanz des Morgenlichts, das immer heller leuchtet bis zur vollen Tageshöhe.
Hanyar adali kamar fitowar rana ce, sai ƙara haske take yi, har ta kai tsaka.
19 Der Weg der Gottlosen ist wie dunkle Nacht; sie gewahren nicht, worüber sie straucheln.
Amma hanyar mugaye kamar zurfin duhu ne; ba sa sanin abin da ya sa suke tuntuɓe.
20 Mein Sohn, merke auf meine Worte, leihe meinen Reden dein Ohr!
Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa, ka saurara sosai ga kalmomina.
21 Laß sie deinen Augen nie entschwinden, bewahre sie im Innersten deines Herzens!
Kada ka bari su rabu da kai, ka kiyaye su a cikin zuciyarka;
22 Denn Leben sind sie für jeden, der sie erfaßt, und heilsame Arznei für seinen ganzen Leib.
gama rai ne ga waɗanda suke nemansu da kuma lafiya ga dukan jikin mutum.
23 Mehr als alles, was man zu bewachen hat, behüte dein Herz; denn von ihm hängt das Leben ab.
Fiye da kome duka, ka tsare zuciyarka, gama maɓulɓulan ruwan rijiyar rai ne.
24 Tu Falschheit des Mundes von dir ab und laß Lug und Trug fern von deinen Lippen sein!
Ka kau da muguwar magana daga bakinka; ka yi nesa da magana marar kyau daga leɓunanka.
25 Dann können deine Augen geradeaus schauen und deine Augenlider frei vor dich hinblicken.
Bari idanunka su dubi gaba sosai, ka kafa idanunka kai tsaye a gabanka.
26 Laß deinen Fuß auf gerader Bahn gehen und alle deine Wege fest gerichtet sein!
Ka san inda ƙafafunka suke takawa ka bi hanyoyin da suke daram kawai.
27 Weiche nicht nach rechts noch nach links ab; halte deinen Fuß vom Bösen fern!
Kada ka kauce dama ko hagu; ka kiyaye ƙafarka daga mugunta.

< Sprueche 4 >