< Job 12 >

1 Da antwortete Hiob folgendermaßen:
Sai Ayuba ya amsa,
2 »Wahrhaftig, ihr seid das Volk, und mit euch wird die Weisheit aussterben!
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 Ich besitze auch Verstand ebensogut wie ihr: ich stehe hinter euch nicht zurück; wem sollten auch derartige Dinge unbekannt sein?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Dem eigenen Freunde muß ich zum Spott dienen, ich, der ich vordem Gott angerufen und auch Erhörung gefunden habe! Zum Spott muß der Gerechte, der Fromme dienen!
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Dem Unglück gebührt Verachtung nach der Ansicht des sich sicher Fühlenden: ein Stoß noch denen, deren Fuß bereits wankt!
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 In Ruhe liegen die Zelte von Gewalttätigen da, und in Sicherheit leben die, welche Gott Trotz bieten, ein jeder, der seinen Gott in seiner Faust führt.«
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 »Aber frage doch das Vieh, das wird dich’s lehren, und die Vögel des Himmels, die werden dir’s kundtun;
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 oder betrachte (den Wurm auf der) Erde, er wird dich’s lehren, und die Fische des Meeres werden dir’s bezeugen:
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 wer von diesen allen wüßte nicht, daß die Hand des HERRN diese Welt geschaffen hat,
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 er, in dessen Hand die Seele aller lebenden Geschöpfe liegt und der Odem eines jeden Menschenwesens?
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Soll nicht das Ohr die Worte prüfen, gleichwie der Gaumen sich die Speisen kostend auswählt?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 ›Bei den Greisen soll die Weisheit wohnen, und langes Leben Einsicht verleihen?‹
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Nein, bei ihm wohnt Weisheit und Stärke, sein ist der Rat und die Einsicht!«
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 »Siehe, wenn er niederreißt, so wird nicht wieder aufgebaut; wen er einkerkert, dem wird nicht wieder aufgetan.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Siehe, wenn er die Wasser hemmt, so versiegen sie, und wenn er sie entfesselt, so wühlen sie die Erde um.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 Bei ihm ist Kraft und vollkommenes Wissen: ihm fällt der Irrende wie der Irreführende in die Hände.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Er läßt Ratsherren als Barfüßige hinwegziehen und erweist Richter als Toren;
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 die Zwingherrschaft von Königen löst er auf und schlingt ihnen einen Strick um die eigenen Hüften;
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Priester führt er als Barfüßige hinweg und bringt die im Amt Ergrauten zu Fall;
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 erprobten Wortführern entzieht er die Rede und benimmt den Greisen das gesunde Urteil;
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 über Edle gießt er Schande aus und löst den Schwertgurt von Gewalthabern;
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Tiefverborgenes enthüllt er aus dem Dunkel heraus und zieht finstere Nacht ans Licht hervor;
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 er läßt Völker groß aufwachsen und vernichtet sie wieder; er breitet Völker weit aus und läßt sie dann verschleppen;
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 er raubt den Volkshäuptern des Landes den Verstand und läßt sie umherirren in pfadloser Einöde,
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 daß sie in lichtloser Finsternis tappen, und er läßt sie umherirren wie Trunkene.«
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >