< 1 Mose 5 >

1 Dies ist die Geschlechtstafel Adams: Am Tage, als Gott den Adam schuf, gestaltete er ihn nach Gottes Ebenbild;
Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
2 als Mann und Weib schuf er sie und segnete sie und gab ihnen den Namen »Mensch« damals, als sie geschaffen wurden.
Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
3 Adam aber war 130 Jahre alt, als ihm ein Sohn geboren wurde, der ihm als sein Abbild glich und den er Seth nannte.
Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
4 Nach der Geburt Seths lebte Adam noch 800 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
5 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Adams 930 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
6 Als Seth 105 Jahre alt war, wurde ihm Enos geboren.
Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
7 Nach der Geburt des Enos lebte Seth noch 807 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
8 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Seths 912 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
9 Als Enos 90 Jahre alt war, wurde ihm Kenan geboren.
Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
10 Nach der Geburt Kenans lebte Enos noch 815 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
11 Demnach betrug die ganze Lebenszeit des Enos 905 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
12 Als Kenan 70 Jahre alt war, wurde ihm Mahalalel geboren.
Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
13 Nach der Geburt Mahalalels lebte Kenan noch 840 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
14 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Kenans 910 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
15 Als Mahalalel 65 Jahre alt war, wurde ihm Jered geboren.
Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
16 Nach der Geburt Jereds lebte Mahalalel noch 830 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
17 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Mahalalels 895 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
18 Als Jered 162 Jahre alt war, wurde ihm Henoch geboren.
Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
19 Nach der Geburt Henochs lebte Jered noch 800 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Jereds 962 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
21 Als Henoch 65 Jahre alt war, wurde ihm Methusalah geboren.
Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
22 Henoch wandelte mit Gott; er lebte nach der Geburt Methusalahs noch 300 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
23 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Henochs 365 Jahre.
Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
24 Henoch wandelte mit Gott und war plötzlich nicht mehr da, denn Gott hatte ihn hinweggenommen. –
Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
25 Als Methusalah 187 Jahre alt war, wurde ihm Lamech geboren.
Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
26 Nach der Geburt Lamechs lebte Methusalah noch 782 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
27 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Methusalahs 969 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
28 Als Lamech 182 Jahre alt war, wurde ihm ein Sohn geboren,
Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
29 den er Noah nannte; »denn«, sagte er, »dieser wird uns Trost verschaffen bei unserer Arbeit und bei der Mühsal, die unsere Hände durch den Acker haben, den der HERR verflucht hat«.
Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
30 Nach der Geburt Noahs lebte Lamech noch 595 Jahre und hatte Söhne und Töchter.
Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
31 Demnach betrug die ganze Lebenszeit Lamechs 777 Jahre; dann starb er. –
Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
32 Als Noah 500 Jahre alt war, wurden ihm seine Söhne Sem, Ham und Japheth geboren.
Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.

< 1 Mose 5 >