< 1 Chronik 24 >

1 Was sodann die Nachkommen Aarons betrifft, so waren ihre Abteilungen folgende: Die Söhne Aarons waren: Nadab und Abihu, Eleasar und Ithamar.
Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
2 Nadab und Abihu starben jedoch vor ihrem Vater, ohne Söhne zu hinterlassen; daher übten Eleasar und Ithamar den Priesterdienst allein aus.
Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
3 David teilte sie nun, im Einvernehmen mit Zadok von den Nachkommen Eleasars und mit Ahimelech von den Nachkommen Ithamars, in Klassen ein je nach ihrem Amt bei ihrer Dienstleistung.
Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
4 Dabei stellte es sich nun heraus, daß die Nachkommen Eleasars an Familienhäuptern zahlreicher waren als die Nachkommen Ithamars; daher teilte man sie so ab, daß auf die Nachkommen Eleasars sechzehn, auf die Nachkommen Ithamars acht Familienhäupter kamen.
Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
5 Man teilte sie aber, die einen wie die anderen, durch Lose ab; denn sowohl unter Eleasars als auch unter Ithamars Nachkommen gab es ›Fürsten des Heiligtums‹ und ›Fürsten Gottes‹;
Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
6 und Semaja, der Sohn Nethaneels, der Schriftführer unter den Leviten, schrieb sie in Gegenwart des Königs und der Fürsten sowie des Priesters Zadok und Ahimelechs, des Sohnes Abjathars, und der Familienhäupter der Priester und der Leviten auf: je eine Familie wurde für Ithamar ausgelost, und dann wurde je zweimal eine für Eleasar ausgelost.
Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
7 Das erste Los fiel auf Jojarib, das zweite auf Jedaja,
Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
8 das dritte auf Harim, das vierte auf Seorim,
na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
9 das fünfte auf Malchia, das sechste auf Mijjamin,
na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
10 das siebte auf Hakkoz, das achte auf Abia,
na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
11 das neunte auf Jesua, das zehnte auf Sechanja,
na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
12 das elfte auf Eljasib, das zwölfte auf Jakim,
na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
13 das dreizehnte auf Huppa, das vierzehnte auf Jesebab,
na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
14 das fünfzehnte auf Bilga, das sechzehnte auf Immer,
na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
15 das siebzehnte auf Hesir, das achtzehnte auf Happizzez,
na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
16 das neunzehnte auf Pethahja, das zwanzigste auf Jeheskel,
na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
17 das einundzwanzigste auf Jachin, das zweiundzwanzigste auf Gamul,
na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
18 das dreiundzwanzigste auf Delaja, das vierundzwanzigste auf Maasja.
na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
19 Dies war ihre Klassenordnung für ihren Dienst, damit sie entsprechend der durch ihren Ahnherrn Aaron für sie bestimmten Verordnung in den Tempel des HERRN einträten, wie der HERR, der Gott Israels, ihm geboten hatte.
Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
20 Was aber die übrigen Nachkommen Levis betrifft, so war von den Nachkommen Amrams Subael da, von den Nachkommen Subaels Jehdeja;
Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
21 von den Nachkommen Rehabjas war Jissia das Oberhaupt. –
Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
22 Von den Jizhariten: Selomoth, von den Nachkommen Selomoths: Jahath. –
Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
23 Die Nachkommen Hebrons waren: Jerija das Oberhaupt, Amarja der zweite, Jahasiel der dritte, Jekameam der vierte. –
’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
24 Die Nachkommen Ussiels waren: Micha; von den Nachkommen Michas: Samir.
Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
25 Michas Bruder war Jissia; von den Nachkommen Jissias: Sacharja. –
Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
26 Die Nachkommen Meraris waren: Mahli und Musi und die Nachkommen seines Sohnes Jaasia.
’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
27 Die Nachkommen Meraris von seinem Sohne Ussia waren: Soham, Sakkur und Ibri;
’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
28 von Mahli: Eleasar, der aber keine Söhne hatte, und Kis;
Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
29 von Kis: die Söhne des Kis: Jerahmeel.
Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
30 Die Nachkommen Musis waren: Mahli, Eder und Jerimoth. Dies waren die Nachkommen der Leviten nach ihren Familien. –
Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
31 Auch sie wurden ausgelost ganz wie ihre Stammesgenossen, die Nachkommen Aarons, in Gegenwart des Königs David und Zadoks und Ahimelechs sowie der Familienhäupter der Priester und der Leviten, und zwar die Familienhäupter ganz ebenso wie ihre jüngsten Stammesgenossen.
Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.

< 1 Chronik 24 >