< Psalm 85 >
1 Ein Psalm der Kinder Korah, vorzusingen. HERR, der du bist vormals gnädig gewesen deinem Lande und hast die Gefangenen Jakobs erlöst;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
2 der du die Missetat vormals vergeben hast deinem Volk und alle ihre Sünde bedeckt (sela)
Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
3 der du vormals hast allen deinen Zorn aufgehoben und dich gewendet von dem Grimm deines Zorns:
Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
4 tröste uns, Gott, unser Heiland, und laß ab von deiner Ungnade über uns!
Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
5 Willst du denn ewiglich über uns zürnen und deinen Zorn gehen lassen für und für?
Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
6 Willst du uns denn nicht wieder erquicken, daß sich dein Volk über dich freuen möge?
Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
7 HERR, erzeige uns deine Gnade und hilf uns!
Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
8 Ach, daß ich hören sollte, was Gott der HERR redet; daß er Frieden zusagte seinem Volk und seinen Heiligen, auf daß sie nicht auf eine Torheit geraten!
Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
9 Doch ist ja seine Hilfe nahe denen, die ihn fürchten, daß in unserm Lande Ehre wohne;
Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
10 daß Güte und Treue einander begegnen, Gerechtigkeit und Friede sich küssen;
Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
11 daß Treue auf der Erde wachse und Gerechtigkeit vom Himmel schaue;
Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
12 daß uns auch der HERR Gutes tue und unser Land sein Gewächs gebe;
Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
13 daß Gerechtigkeit weiter vor ihm bleibe und im Schwange gehe.
Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.