< Psalm 66 >

1 Ein Psalmlied, vorzusingen. Jauchzet Gott, alle Lande!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Lobsinget zu Ehren seinem Namen; rühmet ihn herrlich!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Sprechet zu Gott: “Wie wunderbar sind deine Werke! es wird deinen Feinden fehlen vor deiner großen Macht.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Alles Land bete dich an und lobsinge dir, lobsinge deinem Namen.” (Sela)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Kommet her und sehet an die Werke Gottes, der so wunderbar ist in seinem Tun unter den Menschenkindern.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Er verwandelt das Meer ins Trockene, daß man zu Fuß über das Wasser ging; dort freuten wir uns sein.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Er herrscht mit seiner Gewalt ewiglich; seine Augen schauen auf die Völker. Die Abtrünnigen werden sich nicht erhöhen können. (Sela)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Lobet, ihr Völker, unsern Gott; lasset seinen Ruhm weit erschallen,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 der unsre Seelen im Leben erhält und läßt unsre Füße nicht gleiten.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Denn, Gott, du hast uns versucht und geläutert wie das Silber geläutert wird;
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 du hast uns lassen in den Turm werfen; du hast auf unsere Lenden eine Last gelegt;
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 du hast Menschen lassen über unser Haupt fahren; wir sind in Feuer und Wasser gekommen: aber du hast uns ausgeführt und erquickt.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Darum will ich mit Brandopfern gehen in dein Haus und dir meine Gelübde bezahlen,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 wie ich meine Lippen habe aufgetan und mein Mund geredet hat in meiner Not.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Ich will dir Brandopfer bringen von feisten Schafen samt dem Rauch von Widdern; ich will opfern Rinder mit Böcken. (Sela)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Kommet her, höret zu alle, die ihr Gott fürchtet; ich will erzählen, was er an meiner Seele getan hat.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Zu ihm rief ich mit meinem Munde, und pries ihn mit meiner Zunge.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Wo ich Unrechtes vorhätte in meinem Herzen, so würde der Herr nicht hören;
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 aber Gott hat mich erhört und gemerkt auf mein Flehen.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Gelobt sei Gott, der mein Gebet nicht verwirft noch seine Güte von mir wendet.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psalm 66 >