< Psalm 50 >

1 Ein Psalm Asaphs. Gott, der HERR, der Mächtige, redet und ruft der Welt vom Aufgang der Sonne bis zu ihrem Niedergang.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Aus Zion bricht an der schöne Glanz Gottes.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Unser Gott kommt und schweigt nicht. Fressend Feuer geht vor ihm her und um ihn her ist ein großes Wetter.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Er ruft Himmel und Erde, daß er sein Volk richte:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 “Versammelt mir meine Heiligen, die den Bund mit mir gemacht haben beim Opfer.”
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Und die Himmel werden seine Gerechtigkeit verkündigen; denn Gott ist Richter. (Sela)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 “Höre, mein Volk, laß mich reden; Israel, laß mich unter dir zeugen: Ich, Gott, bin dein Gott.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Deines Opfers halber strafe ich dich nicht, sind doch deine Brandopfer immer vor mir.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Ich will nicht von deinem Hause Farren nehmen noch Böcke aus deinen Ställen.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Denn alle Tiere im Walde sind mein und das Vieh auf den Bergen, da sie bei tausend gehen.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Ich kenne alle Vögel auf den Bergen, und allerlei Tier auf dem Feld ist vor mir.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Wo mich hungerte, wollte ich dir nicht davon sagen; denn der Erdboden ist mein und alles, was darinnen ist.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Meinst du, daß ich Ochsenfleisch essen wolle oder Bocksblut trinken?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Opfere Gott Dank und bezahle dem Höchsten deine Gelübde
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 und rufe mich an in der Not, so will ich dich erretten, so sollst du mich preisen.”
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Aber zum Gottlosen spricht Gott: “Was verkündigst du meine Rechte und nimmst meinen Bund in deinen Mund,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 so du doch Zucht hassest und wirfst meine Worte hinter dich?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Wenn du einen Dieb siehst, so läufst du mit ihm und hast Gemeinschaft mit den Ehebrechern.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Deinen Mund lässest du Böses reden, und deine Zunge treibt Falschheit.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Du sitzest und redest wider deinen Bruder; deiner Mutter Sohn verleumdest du.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Das tust du, und ich schweige; da meinst du, ich werde sein gleichwie du. Aber ich will dich strafen und will dir's unter Augen stellen.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Merket doch das, die ihr Gottes vergesset, daß ich nicht einmal hinraffe und sei kein Retter da.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Wer Dank opfert, der preiset mich; und da ist der Weg, daß ich ihm zeige das Heil Gottes.”
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psalm 50 >