< Psalm 37 >
1 Ein Psalm Davids. Erzürne dich nicht über die Bösen; sei nicht neidisch auf die Übeltäter.
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 Denn wie das Gras werden sie bald abgehauen, und wie das grüne Kraut werden sie verwelken.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Hoffe auf den HERRN und tue Gutes; bleibe im Lande und nähre dich redlich.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Habe Deine Lust am HERRN; der wird dir geben, was dein Herz wünschet.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Befiehl dem HERRN deine Wege und hoffe auf ihn; er wird's wohl machen
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 und wird deine Gerechtigkeit hervorbringen wie das Licht und dein Recht wie den Mittag.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Sei stille dem HERRN und warte auf ihn; erzürne dich nicht über den, dem sein Mutwille glücklich fortgeht.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Steh ab vom Zorn und laß den Grimm, erzürne dich nicht, daß du nicht auch übel tust.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 Denn die Bösen werden ausgerottet; die aber des HERRN harren, werden das Land erben.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Es ist noch um ein kleines, so ist der Gottlose nimmer; und wenn du nach seiner Stätte sehen wirst, wird er weg sein.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 Aber die Elenden werden das Land erben und Lust haben in großem Frieden.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 Der Gottlose droht dem Gerechten und beißt seine Zähne zusammen über ihn.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 Aber der Herr lacht sein; denn er sieht, daß sein Tag kommt.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 Die Gottlosen ziehen das Schwert aus und spannen ihren Bogen, daß sie fällen den Elenden und Armen und schlachten die Frommen.
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Aber ihr Schwert wird in ihr Herz gehen, und ihr Bogen wird zerbrechen.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Das wenige, das ein Gerechter hat, ist besser als das große Gut vieler Gottlosen.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 Denn der Gottlosen Arm wird zerbrechen; aber der HERR erhält die Gerechten.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 Der HERR kennt die Tage der Frommen, und ihr Gut wird ewiglich bleiben.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 Sie werden nicht zu Schanden in der bösen Zeit, und in der Teuerung werden sie genug haben.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 Denn die Gottlosen werden umkommen; und die Feinde des HERRN, wenn sie gleich sind wie köstliche Aue, werden sie doch vergehen, wie der Rauch vergeht.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 Der Gottlose borgt und bezahlt nicht; der Gerechte aber ist barmherzig und gibt.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 Denn seine Gesegneten erben das Land; aber seine Verfluchten werden ausgerottet.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 Von dem HERRN wird solches Mannes Gang gefördert, und er hat Lust an seinem Wege.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Fällt er, so wird er nicht weggeworfen; denn der HERR hält ihn bei der Hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Ich bin jung gewesen und alt geworden und habe noch nie gesehen den Gerechten verlassen oder seinen Samen nach Brot gehen.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 Er ist allezeit barmherzig und leihet gerne, und sein Same wird gesegnet sein.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Laß vom Bösen und tue Gutes und bleibe wohnen immerdar.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 Denn der HERR hat das Recht lieb und verläßt seine Heiligen nicht; ewiglich werden sie bewahrt; aber der Gottlosen Same wird ausgerottet.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 Die Gerechten erben das Land und bleiben ewiglich darin.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 Der Mund des Gerechten redet die Weisheit, und seine Zunge lehrt das Recht.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 Das Gesetz seines Gottes ist in seinem Herzen; seine Tritte gleiten nicht.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 Der Gottlose lauert auf den Gerechten und gedenkt ihn zu töten.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Aber der HERR läßt ihn nicht in seinen Händen und verdammt ihn nicht, wenn er verurteilt wird.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Harre auf den HERRN und halte seinen Weg, so wird er dich erhöhen, daß du das Land erbest; du wirst es sehen, daß die Gottlosen ausgerottet werden.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 Ich habe gesehen einen Gottlosen, der war trotzig und breitete sich aus und grünte wie ein Lorbeerbaum.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Da man vorüberging, siehe, da war er dahin; ich fragte nach ihm, da ward er nirgend gefunden.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Bleibe fromm und halte dich recht; denn solchem wird's zuletzt wohl gehen.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 Die Übertreter aber werden vertilgt miteinander, und die Gottlosen werden zuletzt ausgerottet.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 Aber der HERR hilft den Gerechten; der ist ihre Stärke in der Not.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 Und der HERR wird ihnen beistehen und wird sie erretten; er wird sie von dem Gottlosen erretten und ihnen helfen; denn sie trauen auf ihn.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.