< Psalm 148 >

1 Halleluja! Lobet im Himmel den HERRN; lobet ihn in der Höhe!
Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
2 Lobet ihn, alle seine Engel; lobet ihn, all sein Heer!
Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
3 Lobet ihn, Sonne und Mond; lobet ihn, alle leuchtenden Sterne!
Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
4 Lobet ihn, ihr Himmel allenthalben und die Wasser, die oben am Himmel sind!
Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
5 Die sollen loben den Namen des HERRN; denn er gebot, da wurden sie geschaffen.
Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
6 Er hält sie immer und ewiglich; er ordnet sie, daß sie nicht anders gehen dürfen.
Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
7 Lobet den HERRN auf Erden, ihr Walfische und alle Tiefen;
Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
8 Feuer, Hagel, Schnee und Dampf, Strumwinde, die sein Wort ausrichten;
walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
9 Berge und alle Hügel, fruchtbare Bäume und alle Zedern;
ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
10 Tiere und alles Vieh, Gewürm und Vögel;
namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
11 ihr Könige auf Erden und alle Völker, Fürsten und alle Richter auf Erden;
sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
12 Jünglinge und Jungfrauen, Alte mit den Jungen!
samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
13 Die sollen loben den Namen des HERRN; denn sein Name allein ist hoch, sein Lob geht, soweit Himmel und Erde ist.
Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
14 Und erhöht das Horn seines Volkes. Alle Heiligen sollen loben, die Kinder Israel, das Volk, das ihm dient. Halleluja!
Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.

< Psalm 148 >