< Psalm 147 >

1 Lobet den HERRN! denn unsern Gott loben, das ist ein köstlich Ding; solch Lob ist lieblich und schön.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 Der HERR baut Jerusalem und bringt zusammen die Verjagten Israels.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Er heilt, die zerbrochnes Herzens sind, und verbindet ihre Schmerzen.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Er zählt die Sterne und nennt sie alle mit Namen.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Der HERR ist groß und von großer Kraft; und ist unbegreiflich, wie er regiert.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Der Herr richtet auf die Elenden und stößt die Gottlosen zu Boden.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Singet umeinander dem HERRN mit Dank und lobet unsern Gott mit Harfen,
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 der den Himmel mit Wolken verdeckt und gibt Regen auf Erden; der Gras auf Bergen wachsen läßt;
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 der dem Vieh sein Futter gibt, den jungen Raben, die ihn anrufen.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Er hat nicht Lust an der Stärke des Rosses noch Gefallen an eines Mannes Schenkeln.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Der HERR hat Gefallen an denen, die ihn fürchten, die auf seine Güte hoffen.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Preise, Jerusalem, den HERRN; lobe Zion, deinen Gott!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Denn er macht fest die Riegel deiner Tore und segnet deine Kinder drinnen.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Er schafft deinen Grenzen Frieden und sättigt dich mit dem besten Weizen.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Er sendet seine Rede auf Erden; sein Wort läuft schnell.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Er gibt Schnee wie Wolle, er streut Reif wie Asche.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Er wirft seine Schloßen wie Bissen; wer kann bleiben vor seinem Frost?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Er spricht, so zerschmilzt es; er läßt seinen Wind wehen, so taut es auf.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 Er zeigt Jakob sein Wort, Israel seine Sitten und Rechte.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 So tut er keinen Heiden, noch läßt er sie wissen seine Rechte. Halleluja!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psalm 147 >