< Psalm 139 >
1 Ein Psalm Davids, vorzusingen. HERR, Du erforschest mich und kennest mich.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 Ich sitze oder stehe auf, so weißt du es; du verstehst meine Gedanken von ferne.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 Ich gehe oder liege, so bist du um mich und siehst alle meine Wege.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Denn siehe, es ist kein Wort auf meiner Zunge, das du, HERR, nicht alles wissest.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Von allen Seiten umgibst du mich und hältst deine Hand über mir.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 Solche Erkenntnis ist mir zu wunderbar und zu hoch; ich kann sie nicht begreifen.
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Wo soll ich hin gehen vor deinem Geist, und wo soll ich hin fliehen vor deinem Angesicht?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 Führe ich gen Himmel, so bist du da. Bettete ich mir in die Hölle, siehe, so bist du auch da. (Sheol )
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
9 Nähme ich Flügel der Morgenröte und bliebe am äußersten Meer,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 so würde mich doch deine Hand daselbst führen und deine Rechte mich halten.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 Spräche ich: Finsternis möge mich decken! so muß die Nacht auch Licht um mich sein.
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 Denn auch Finsternis ist nicht finster bei dir, und die Nacht leuchtet wie der Tag, Finsternis ist wie das Licht.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 Denn du hast meine Nieren bereitet und hast mich gebildet im Mutterleib.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 Ich danke dir dafür, daß ich wunderbar gemacht bin; wunderbar sind deine Werke, und das erkennt meine Seele wohl.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 Es war dir mein Gebein nicht verhohlen, da ich im Verborgenen gemacht ward, da ich gebildet ward unten in der Erde.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Deine Augen sahen mich, da ich noch unbereitet war, und alle Tage waren auf dein Buch geschrieben, die noch werden sollten, als derselben keiner da war.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 Aber wie köstlich sind vor mir, Gott, deine Gedanken! Wie ist ihrer so eine große Summe!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 Sollte ich sie zählen, so würde ihrer mehr sein denn des Sandes. Wenn ich aufwache, bin ich noch bei dir.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 Ach Gott, daß du tötetest die Gottlosen, und die Blutgierigen von mir weichen müßten!
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 Denn sie reden von dir lästerlich, und deine Feinde erheben sich ohne Ursache.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Ich hasse ja, HERR, die dich hassen, und es verdrießt mich an ihnen, daß sie sich wider dich setzen.
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 Ich hasse sie im rechten Ernst; sie sind mir zu Feinden geworden.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Erforsche mich, Gott, und erfahre mein Herz; prüfe mich und erfahre, wie ich's meine.
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 Und siehe, ob ich auf bösem Wege bin, und leite mich auf ewigem Wege.
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.