< Psalm 135 >

1 Halleluja! Lobet den Namen des HERRN, lobet, ihr Knechte des HERRN,
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 die ihr stehet im Hause des HERRN, in den Höfen des Hauses unsers Gottes!
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Lobet den HERRN, denn der HERR ist freundlich; lobsinget seinem Namen, denn er ist lieblich!
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Denn der HERR hat sich Jakob erwählt, Israel zu seinem Eigentum.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Denn ich weiß, daß der HERR groß ist und unser HERR vor allen Göttern.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Alles, was er will, das tut er, im Himmel und auf Erden, im Meer und in allen Tiefen;
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 der die Wolken läßt aufsteigen vom Ende der Erde, der die Blitze samt dem Regen macht, der den Wind aus seinen Vorratskammern kommen läßt;
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 der die Erstgeburten schlug in Ägypten, beider, der Menschen und des Viehes,
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 und ließ Zeichen und Wunder kommen über dich, Ägyptenland, über Pharao und alle seine Knechte;
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 der viele Völker schlug und tötete mächtige Könige:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon, der Amoriter König, und Og, den König von Basan, und alle Königreiche in Kanaan;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 und gab ihr Land zum Erbe, zum Erbe seinem Volk Israel.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 HERR, dein Name währet ewiglich; dein Gedächtnis, HERR, währet für und für.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Denn der HERR wird sein Volk richten und seinen Knechten gnädig sein.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Der Heiden Götzen sind Silber und Gold, von Menschenhänden gemacht.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Sie haben Mäuler, und reden nicht; sie haben Augen, und sehen nicht;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 sie haben Ohren, und hören nicht; auch ist kein Odem in ihrem Munde.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Die solche machen, sind gleich also, alle, die auf solche hoffen.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Das Haus Israel lobe den HERRN! Lobet den HERRN, ihr vom Hause Aaron!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Ihr vom Hause Levi, lobet den HERRN! Die ihr den HERRN fürchtet, lobet den HERRN!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Gelobet sei der HERR aus Zion, der zu Jerusalem wohnt! Halleluja!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalm 135 >