< Psalm 132 >

1 Ein Lied im höhern Chor. Gedenke, HERR, an David und all sein Leiden,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 der dem HERRN schwur und gelobte dem Mächtigen Jakobs:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 “Ich will nicht in die Hütte meines Hauses gehen noch mich aufs Lager meines Bettes legen,
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 ich will meine Augen nicht schlafen lassen noch meine Augenlider schlummern,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 bis ich eine Stätte finde für den HERRN, zur Wohnung des Mächtigen Jakobs.”
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Siehe, wir hörten von ihr in Ephratha; wir haben sie gefunden auf dem Felde des Waldes.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Wir wollen in seine Wohnung gehen und anbeten vor seinem Fußschemel.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 HERR, mache dich auf zu deiner Ruhe, du und die Lade deiner Macht!
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Deine Priester laß sich kleiden mit Gerechtigkeit und deine Heiligen sich freuen.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Wende nicht weg das Antlitz deines Gesalbten um deines Knechtes David willen.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Der HERR hat David einen wahren Eid geschworen, davon wird er sich nicht wenden: “Ich will dir auf deinen Stuhl setzen die Frucht deines Leibes.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Werden deine Kinder meinen Bund halten und mein Zeugnis, das ich sie lehren werde, so sollen auch ihre Kinder auf deinem Stuhl sitzen ewiglich.”
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Denn der HERR hat Zion erwählt und hat Lust, daselbst zu wohnen.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 “Dies ist meine Ruhe ewiglich, hier will ich wohnen; denn es gefällt mir wohl.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Ich will ihre Speise segnen und ihren Armen Brot genug geben.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Ihre Priester will ich mit Heil kleiden, und ihre Heiligen sollen fröhlich sein.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Daselbst soll aufgehen das Horn Davids; ich habe meinen Gesalbten eine Leuchte zugerichtet.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Seine Feinde will ich mit Schanden kleiden; aber über ihm soll blühen seine Krone.”
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”

< Psalm 132 >