< Psalm 119 >
1 Wohl denen, die ohne Tadel leben, die im Gesetz des HERRN wandeln!
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Wohl denen, die seine Zeugnisse halten, die ihn von ganzem Herzen suchen!
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Denn welche auf seinen Wegen wandeln, die tun kein Übel.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Du hast geboten, fleißig zu halten deine Befehle.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Oh daß mein Leben deine Rechte mit ganzem Ernst hielte!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Wenn ich schaue allein auf deine Gebote, so werde ich nicht zu Schanden.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Ich danke dir von Herzen, daß du mich lehrst die Rechte deiner Gerechtigkeit.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Deine Rechte will ich halten; verlaß mich nimmermehr.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Wie wird ein Jüngling seinen Weg unsträflich gehen? Wenn er sich hält nach deinen Worten.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Ich suche dich von ganzem Herzen; laß mich nicht abirren von deinen Geboten.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Ich behalte dein Wort in meinem Herzen, auf daß ich nicht wieder dich sündige.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Gelobt seist du, HERR! Lehre mich deine Rechte!
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Ich will mit meinen Lippen erzählen alle Rechte deines Mundes.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Ich freue mich des Weges deiner Zeugnisse wie über allerlei Reichtum.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Ich rede von dem, was du befohlen hast, und schaue auf deine Wege.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Ich habe Lust zu deinen Rechten und vergesse deiner Worte nicht.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Tue wohl deinem Knecht, daß ich lebe und dein Wort halte.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Öffne mir die Augen, daß ich sehe die Wunder an deinem Gesetz.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Ich bin ein Gast auf Erden; verbirg deine Gebote nicht vor mir.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Meine Seele ist zermalmt vor Verlangen nach deinen Rechten allezeit.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Du schiltst die Stolzen; verflucht sind, die von deinen Geboten abirren.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Wende von mir Schmach und Verachtung; denn ich halte deine Zeugnisse.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Es sitzen auch die Fürsten und reden wider mich; aber dein Knecht redet von deinen Rechten.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Ich habe Lust zu deinen Zeugnissen; die sind meine Ratsleute.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Meine Seele liegt im Staube; erquicke mich nach deinem Wort.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Ich erzähle meine Wege, und du erhörst mich; lehre mich deine Rechte.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Unterweise mich den Weg deiner Befehle, so will ich reden von deinen Wundern.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Ich gräme mich, daß mir das Herz verschmachtet; stärke mich nach deinem Wort.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Wende von mir den falschen Weg und gönne mir dein Gesetz.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 Ich habe den Weg der Wahrheit erwählt; deine Rechte habe ich vor mich gestellt.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Ich hange an deinen Zeugnissen; HERR, laß mich nicht zu Schanden werden!
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Wenn du mein Herz tröstest, so laufe ich den Weg deiner Gebote.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Zeige mir, HERR, den Weg deiner Rechte, daß ich sie bewahre bis ans Ende.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Unterweise mich, daß ich bewahre dein Gesetz und halte es von ganzem Herzen.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Führe mich auf dem Steige deiner Gebote; denn ich habe Lust dazu.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Neige mein Herz zu deinen Zeugnissen, und nicht zum Geiz.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Wende meine Augen ab, daß sie nicht sehen nach unnützer Lehre; sondern erquicke mich auf deinem Wege.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Laß deinen Knecht dein Gebot fest für dein Wort halten, daß ich mich nicht fürchte.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Wende von mir die Schmach, die ich scheue; denn deine Rechte sind lieblich.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Siehe, ich begehre deiner Befehle; erquicke mich mit deiner Gerechtigkeit.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 HERR, laß mir deine Gnade widerfahren, deine Hilfe nach deinem Wort,
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 daß ich antworten möge meinem Lästerer; denn ich verlasse mich auf dein Wort.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Und nimm ja nicht von meinem Munde das Wort der Wahrheit; denn ich hoffe auf deine Rechte.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Ich will dein Gesetz halten allewege, immer und ewiglich.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Und ich wandle fröhlich; denn ich suche deine Befehle.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Ich rede von deinen Zeugnissen vor Königen und schäme mich nicht
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 und habe Lust an deinen Geboten, und sie sind mir lieb,
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 und hebe meine Hände auf zu deinen Geboten, die mir lieb sind, und rede von deinen Rechten.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Gedenke deinem Knechte an dein Wort, auf welches du mich lässest hoffen.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Das ist mein Trost in meinem Elend; denn dein Wort erquickt mich.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Die Stolzen haben ihren Spott an mir; dennoch weiche ich nicht von deinem Gesetz.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 HERR, wenn ich gedenke, wie du von der Welt her gerichtet hast, so werde ich getröstet.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Ich bin entbrannt über die Gottlosen, die dein Gesetz verlassen.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Deine Rechte sind mein Lied in dem Hause meiner Wallfahrt.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 HERR, ich gedenke des Nachts an deinen Namen und halte dein Gesetz.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Das ist mein Schatz, daß ich deine Befehle halte.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Ich habe gesagt: “HERR, das soll mein Erbe sein, daß ich deine Worte halte.”
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Ich flehe vor deinem Angesicht von ganzem Herzen; sei mir gnädig nach deinem Wort.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Ich betrachte meine Wege und kehre meine Füße zu deinen Zeugnissen.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Ich eile und säume mich nicht, zu halten deine Gebote.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Der Gottlosen Rotte beraubt mich; aber ich vergesse deines Gesetzes nicht.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Zur Mitternacht stehe ich auf, dir zu danken für die Rechte deiner Gerechtigkeit.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Ich halte mich zu denen, die dich fürchten und deine Befehle halten.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 HERR, die Erde ist voll deiner Güte; lehre mich deine Rechte.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Du tust Gutes deinem Knechte, HERR, nach deinem Wort.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Lehre mich heilsame Sitten und Erkenntnis; den ich glaube deinen Geboten.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Ehe ich gedemütigt ward, irrte ich; nun aber halte ich dein Wort.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Du bist gütig und freundlich; lehre mich deine Rechte.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Die Stolzen erdichten Lügen über mich; ich aber halte von ganzem Herzen deine Befehle.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Ihr Herz ist dick wie Schmer; ich aber habe Lust an deinem Gesetz.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Es ist mir lieb, daß du mich gedemütigt hast, daß ich deine Rechte lerne.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Das Gesetz deines Mundes ist mir lieber denn viel tausend Stück Gold und Silber.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Deine Hand hat mich gemacht und bereitet; unterweise mich, daß ich deine Gebote lerne.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Die dich fürchten, sehen mich und freuen sich; denn ich hoffe auf dein Wort.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 HERR, ich weiß, daß deine Gerichte recht sind; du hast mich treulich gedemütigt.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Deine Gnade müsse mein Trost sein, wie du deinem Knecht zugesagt hast.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Laß mir deine Barmherzigkeit widerfahren, daß ich lebe; denn ich habe Lust zu deinem Gesetz.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Ach daß die Stolzen müßten zu Schanden werden, die mich mit Lügen niederdrücken! ich aber rede von deinen Befehlen.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Ach daß sich müßten zu mir halten, die dich fürchten und deine Zeugnisse kennen!
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Mein Herz bleibe rechtschaffen in deinen Rechten, daß ich nicht zu Schanden werde.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Meine Seele verlangt nach deinem Heil; ich hoffe auf dein Wort.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Meine Augen sehnen sich nach deinem Wort und sagen: Wann tröstest du mich?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Denn ich bin wie ein Schlauch im Rauch; deiner Rechte vergesse ich nicht.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Wie lange soll dein Knecht warten? Wann willst du Gericht halten über meine Verfolger?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Die Stolzen graben ihre Gruben, sie, die nicht sind nach deinem Gesetz.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Deine Gebote sind eitel Wahrheit. Sie verfolgen mich mit Lügen; hilf mir.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Sie haben mich schier umgebracht auf Erden; ich aber lasse deine Befehle nicht.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Erquicke mich durch deine Gnade, daß ich halte die Zeugnisse deines Mundes.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 HERR, dein Wort bleibt ewiglich, soweit der Himmel ist;
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 deine Wahrheit währet für und für. Du hast die Erde zugerichtet, und sie bleibt stehen.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Es bleibt täglich nach deinem Wort; denn es muß dir alles dienen.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Wo dein Gesetz nicht mein Trost gewesen wäre, so wäre ich vergangen in meinem Elend.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Ich will deine Befehle nimmermehr vergessen; denn du erqickest mich damit.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Ich bin dein, hilf mir! denn ich suche deine Befehle.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Die Gottlosen lauern auf mich, daß sie mich umbringen; ich aber merke auf deine Zeugnisse.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 Ich habe alles Dinges ein Ende gesehen; aber dein Gebot währet.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 Wie habe ich dein Gesetz so lieb! Täglich rede ich davon.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Du machst mich mit deinem Gebot weiser, als meine Feinde sind; denn es ist ewiglich mein Schatz.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Ich bin gelehrter denn alle meine Lehrer; denn deine Zeugnisse sind meine Rede.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Ich bin klüger denn die Alten; denn ich halte deine Befehle.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 Ich wehre meinem Fuß alle bösen Wege, daß ich dein Wort halte.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Ich weiche nicht von deinen Rechten; denn du lehrest mich.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Dein Wort ist meinem Munde süßer denn Honig.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Dein Wort macht mich klug; darum hasse ich alle falschen Wege.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Dein Wort ist meine Fußes Leuchte und ein Licht auf meinem Wege.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Ich schwöre und will's halten, daß ich die Rechte deiner Gerechtigkeit halten will.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Ich bin sehr gedemütigt; HERR, erquicke mich nach deinem Wort!
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Laß dir gefallen, HERR das willige Opfer meines Mundes und lehre mich deine Rechte.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Ich trage meine Seele immer in meinen Händen, und ich vergesse deines Gesetzes nicht.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Die Gottlosen legen mir Stricke; ich aber irre nicht von deinen Befehlen.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Deine Zeugnisse sind mein ewiges Erbe; denn sie sind meines Herzens Wonne.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Ich neige mein Herz, zu tun nach deinen Rechten immer und ewiglich.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Ich hasse die Flattergeister und liebe dein Gesetz.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Du bist mein Schirm und Schild; ich hoffe auf dein Wort.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Weichet von mir, ihr Boshaften! Ich will halten die Gebote meines Gottes.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Erhalte mich durch dein Wort, daß ich lebe; und laß mich nicht zu Schanden werden über meiner Hoffnung.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Stärke mich, daß ich genese, so will ich stets meine Lust haben an deinen Rechten.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Du zertrittst alle, die von deinen Rechten abirren; denn ihre Trügerei ist eitel Lüge.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Du wirfst alle Gottlosen auf Erden weg wie Schlacken; darum liebe ich deine Zeugnisse.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Ich fürchte mich vor dir, daß mir die Haut schaudert, und entsetze mich vor deinen Gerichten.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 Ich halte über Recht und Gerechtigkeit; übergib mich nicht denen, die mir wollen Gewalt tun.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Vertritt du deinen Knecht und tröste ihn; mögen mir die Stolzen nicht Gewalt tun.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Meine Augen sehnen sich nach deinem Heil und nach dem Wort deiner Gerechtigkeit.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Handle mit deinem Knecht nach deiner Gnade und lehre mich deine Rechte.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Ich bin dein Knecht; unterweise mich, daß ich erkenne deine Zeugnisse.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Es ist Zeit, daß der HERR dazutue; sie haben dein Gesetz zerrissen.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Darum liebe ich dein Gebot über Gold und über feines Gold.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Darum halte ich stracks alle deine Befehle; ich hasse allen falschen Weg.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Deine Zeugnisse sind wunderbar; darum hält sie meine Seele.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 Wenn dein Wort offenbar wird, so erfreut es und macht klug die Einfältigen.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Ich sperre meinen Mund auf und lechze nach deinen Geboten; denn mich verlangt darnach.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Wende dich zu mir und sei mir gnädig, wie du pflegst zu tun denen, die deinen Namen lieben.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Laß meinen Gang gewiß sein in deinem Wort und laß kein Unrecht über mich herrschen.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Erlöse mich von der Menschen Frevel, so will ich halten deine Befehle.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Laß dein Antlitz leuchten über deinen Knecht und lehre mich deine Rechte.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Meine Augen fließen mit Wasser, daß man dein Gesetz nicht hält.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 HERR, du bist gerecht, und dein Wort ist recht.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Du hast die Zeugnisse deiner Gerechtigkeit und die Wahrheit hart geboten.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Ich habe mich schier zu Tode geeifert, daß meine Gegner deiner Worte vergessen.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Dein Wort ist wohl geläutert, und dein Knecht hat es lieb.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Ich bin gering und verachtet; ich vergesse aber nicht deiner Befehle.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Deine Gerechtigkeit ist eine ewige Gerechtigkeit, und dein Gesetz ist Wahrheit.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Angst und Not haben mich getroffen; ich habe aber Lust an deinen Geboten.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Die Gerechtigkeit deiner Zeugnisse ist ewig; unterweise mich, so lebe ich.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 Ich rufe von ganzem Herzen; erhöre mich, HERR, daß ich dein Rechte halte.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Ich rufe zu dir; hilf mir, daß ich deine Zeugnisse halte.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Ich komme in der Frühe und schreie; auf dein Wort hoffe ich.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Ich wache auf, wenn's noch Nacht ist, zu sinnen über dein Wort.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Höre meine Stimme nach deiner Gnade; HERR, erquicke mich nach deinen Rechten.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Meine boshaften Verfolger nahen herzu und sind ferne von deinem Gesetz.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 HERR, du bist nahe, und deine Gebote sind eitel Wahrheit.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Längst weiß ich, daß du deine Zeugnisse für ewig gegründet hast.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Siehe mein Elend und errette mich; hilf mir aus, denn ich vergesse deines Gesetzes nicht.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Führe meine Sache und erlöse mich; erquicke mich durch dein Wort.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Das Heil ist ferne von den Gottlosen; denn sie achten deine Rechte nicht.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 HERR, deine Barmherzigkeit ist groß; erquicke mich nach deinen Rechten.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Meiner Verfolger und Widersacher sind viele; ich weiche aber nicht von deinen Zeugnissen.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Ich sehe die Verächter, und es tut mir wehe, daß sie dein Wort nicht halten.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Siehe, ich liebe deine Befehle; HERR, erquicke mich nach deiner Gnade.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 Dein Wort ist nichts denn Wahrheit; alle Rechte deiner Gerechtigkeit währen ewiglich.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Die Fürsten verfolgen mich ohne Ursache, und mein Herz fürchtet sich vor deinen Worten.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Ich freue mich über dein Wort wie einer, der eine große Beute kriegt.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Lügen bin ich gram und habe Greuel daran; aber dein Gesetz habe ich lieb.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Ich lobe dich des Tages siebenmal um der Rechte willen deiner Gerechtigkeit.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Großen Frieden haben, die dein Gesetz lieben; sie werden nicht straucheln.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 HERR, ich warte auf dein Heil und tue nach deinen Geboten.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Meine Seele hält deine Zeugnisse und liebt sie sehr.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Ich halte deine Befehle und deine Zeugnisse; denn alle meine Wege sind vor dir.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 HERR, laß meine Klage vor dich kommen; unterweise mich nach deinem Wort.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Laß mein Flehen vor dich kommen; errette mich nach deinem Wort.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Meine Lippen sollen loben, wenn du mich deine Rechte lehrest.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Meine Zunge soll ihr Gespräch haben von deinem Wort; denn alle deine Gebote sind recht.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Laß mir deine Hand beistehen; denn ich habe erwählt deine Befehle.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 HERR, mich verlangt nach deinem Heil, und ich habe Lust an deinem Gesetz.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Laß meine Seele leben, daß sie dich lobe, und deine Rechte mir helfen.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Ich bin ein verirrtes und verlorenes Schaf. Suche deinen Knecht; denn ich vergesse deiner Gebote nicht.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.