< Psalm 114 >

1 Da Israel aus Ägypten zog, das Haus Jakob aus dem fremden Volk,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 da ward Juda sein Heiligtum, Israel seine Herrschaft.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 Das Meer sah es und floh; der Jordan wandte sich zurück;
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 die Berge hüpften wie die Lämmer, die Hügel wie die jungen Schafe.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 Was war dir, du Meer, daß du flohest, und du, Jordan, daß du dich zurückwandtest,
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 ihr Berge, daß ihr hüpftet wie die Lämmer, ihr Hügel wie die jungen Schafe?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Vor dem HERRN bebte die Erde, vor dem Gott Jakobs,
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 der den Fels wandelte in einen Wassersee und die Steine in Wasserbrunnen.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Psalm 114 >