< Psalm 107 >

1 Danket dem HERRN; denn er ist freundlich, und seine Güte währet ewiglich.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 So sollen sagen, die erlöst sind durch den HERRN, die er aus der Not erlöst hat
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 und die er aus den Ländern zusammengebracht hat vom Aufgang, vom Niedergang, von Mitternacht und vom Meer.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Die irregingen in der Wüste, in ungebahntem Wege, und fanden keine Stadt, da sie wohnen konnten,
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 hungrig und durstig, und ihre Seele verschmachtete;
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 die zum HERRN riefen in ihrer Not, und er errettete sie aus ihren Ängsten
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 und führte sie einen richtigen Weg, daß sie gingen zur Stadt, da sie wohnen konnten:
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 die sollen dem HERRN danken für seine Güte und für seine Wunder, die er an den Menschenkindern tut,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 daß er sättigt die durstige Seele und füllt die hungrige Seele mit Gutem.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Die da sitzen mußten in Finsternis und Dunkel, gefangen in Zwang und Eisen,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 darum daß sie Gottes Geboten ungehorsam gewesen waren und das Gesetz des Höchsten geschändet hatten,
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 dafür ihr Herz mit Unglück geplagt werden mußte, daß sie dalagen und ihnen niemand half;
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 die zum HERRN riefen in ihrer Not, und er half ihnen aus ihren Ängsten
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 und führte sie aus der Finsternis und Dunkel und zerriß ihre Bande:
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 die sollen dem HERRN danken für seine Güte und für seine Wunder, die an den Menschenkindern tut,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 daß er zerbricht eherne Türen und zerschlägt eiserne Riegel.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Die Narren, so geplagt waren um ihrer Übertretung willen und um ihrer Sünden willen,
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 daß ihnen ekelte vor aller Speise und sie todkrank wurden;
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 die riefen zum HERRN in ihrer Not, und er half ihnen aus ihren Ängsten,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 er sandte sein Wort und machte sie gesund und errettete sie, daß sie nicht starben:
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 die sollen dem HERRN danken für seine Güte und für seine Wunder, die er an den Menschenkindern tut,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 und Dank opfern und erzählen seine Werke mit Freuden.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Die mit Schiffen auf dem Meer fuhren und trieben ihren Handel in großen Wassern;
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 die des HERRN Werke erfahren haben und seine Wunder im Meer,
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 wenn er sprach und einen Sturmwind erregte, der die Wellen erhob,
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 und sie gen Himmel fuhren und in den Abgrund fuhren, daß ihre Seele vor Angst verzagte,
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 daß sie taumelten und wankten wie ein Trunkener und wußten keinen Rat mehr;
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 die zum HERRN schrieen in ihrer Not, und er führte sie aus ihren Ängsten
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 und stillte das Ungewitter, daß die Wellen sich legten
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 und sie froh wurden, daß es still geworden war und er sie zu Lande brachte nach ihrem Wunsch:
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 die sollen dem HERRN danken für seine Güte und für seine Wunder, die er an den Menschenkindern tut,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 und ihn bei der Gemeinde preisen und bei den Alten rühmen.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Er machte Bäche trocken und ließ Wasserquellen versiegen,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 daß ein fruchtbar Land zur Salzwüste wurde um der Bosheit willen derer, die darin wohnten.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Er machte das Trockene wiederum wasserreich und im dürren Lande Wasserquellen
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 und hat die Hungrigen dahingesetzt, daß sie eine Stadt zurichten, da sie wohnen konnten,
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 und Äcker besäen und Weinberge pflanzen möchten und die jährlichen Früchte gewönnen.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Und er segnete sie, daß sie sich sehr mehrten, und gab ihnen viel Vieh.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Sie waren niedergedrückt und geschwächt von dem Bösen, das sie gezwungen und gedrungen hatte.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Er schüttete Verachtung auf die Fürsten und ließ sie irren in der Wüste, da kein Weg ist,
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 und schützte den Armen vor Elend und mehrte sein Geschlecht wie eine Herde.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Solches werden die Frommen sehen und sich freuen; und aller Bosheit wird das Maul gestopft werden.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Wer ist weise und behält dies? So werden sie merken, wie viel Wohltaten der HERR erzeigt.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalm 107 >