< Sprueche 8 >

1 Ruft nicht die Weisheit, und die Klugheit läßt sich hören?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Öffentlich am Wege und an der Straße steht sie.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 An den Toren bei der Stadt, da man zur Tür eingeht, schreit sie:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 O ihr Männer, ich schreie zu euch und rufe den Leuten.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Merkt, ihr Unverständigen, auf Klugheit und, ihr Toren, nehmt es zu Herzen!
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Höret, denn ich will reden, was fürstlich ist, und lehren, was recht ist.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Denn mein Mund soll die Wahrheit reden, und meine Lippen sollen hassen, was gottlos ist.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Alle Reden meines Mundes sind gerecht; es ist nichts Verkehrtes noch falsches darin.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Sie sind alle gerade denen, die sie verstehen, und richtig denen, die es annehmen wollen.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Nehmet an meine Zucht lieber denn Silber, und die Lehre achtet höher denn köstliches Gold.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Denn Weisheit ist besser als Perlen; und alles, was man wünschen mag, kann ihr nicht gleichen.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Ich, Weisheit, wohne bei der Klugheit und weiß guten Rat zu geben.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Die Furcht des HERRN haßt das Arge, die Hoffart, den Hochmut und bösen Weg; und ich bin feind dem verkehrten Mund.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Mein ist beides, Rat und Tat; ich habe Verstand und Macht.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Durch mich regieren die Könige und setzen die Ratsherren das Recht.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Durch mich herrschen die Fürsten und alle Regenten auf Erden.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Ich liebe, die mich lieben; und die mich frühe suchen, finden mich.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Reichtum und Ehre ist bei mir, währendes Gut und Gerechtigkeit.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Meine Frucht ist besser denn Gold und feines Gold und mein Ertrag besser denn auserlesenes Silber.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Ich wandle auf dem rechten Wege, auf der Straße des Rechts,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 daß ich wohl versorge, die mich lieben, und ihre Schätze vollmache.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Der HERR hat mich gehabt im Anfang seiner Wege; ehe er etwas schuf, war ich da.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Ich bin eingesetzt von Ewigkeit, von Anfang, vor der Erde.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Da die Tiefen noch nicht waren, da war ich schon geboren, da die Brunnen noch nicht mit Wasser quollen.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Ehe denn die Berge eingesenkt waren, vor den Hügeln war ich geboren,
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 da er die Erde noch nicht gemacht hatte und was darauf ist, noch die Berge des Erdbodens.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Da er die Himmel bereitete, war ich daselbst, da er die Tiefe mit seinem Ziel faßte.
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 Da er die Wolken droben festete, da er festigte die Brunnen der Tiefe,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 da er dem Meer das Ziel setzte und den Wassern, daß sie nicht überschreiten seinen Befehl, da er den Grund der Erde legte:
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 da war ich der Werkmeister bei ihm und hatte meine Lust täglich und spielte vor ihm allezeit
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 und spielte auf seinem Erdboden, und meine Lust ist bei den Menschenkindern.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 So gehorchet mir nun, meine Kinder. Wohl denen, die meine Wege halten!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Höret die Zucht und werdet weise und lasset sie nicht fahren.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Wohl dem Menschen, der mir gehorcht, daß er wache an meiner Tür täglich, daß er warte an den Pfosten meiner Tür.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Wer mich findet, der findet das Leben und wird Wohlgefallen vom HERRN erlangen.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Wer aber an mir sündigt, der verletzt seine Seele. Alle, die mich hassen, lieben den Tod.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Sprueche 8 >