< Job 38 >

1 Und der HERR antwortete Hiob aus dem Wetter und sprach:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Wer ist der, der den Ratschluß verdunkelt mit Worten ohne Verstand?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Gürte deine Lenden wie ein Mann; ich will dich fragen, lehre mich!
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Wo warst du, da ich die Erde gründete? Sage an, bist du so klug!
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Weißt du, wer ihr das Maß gesetzt hat oder wer über sie eine Richtschnur gezogen hat?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Worauf stehen ihre Füße versenkt, oder wer hat ihren Eckstein gelegt,
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 da mich die Morgensterne miteinander lobten und jauchzten alle Kinder Gottes?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Wer hat das Meer mit Türen verschlossen, da es herausbrach wie aus Mutterleib,
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 da ich's mit Wolken kleidete und in Dunkel einwickelte wie in Windeln,
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 da ich ihm den Lauf brach mit meinem Damm und setzte ihm Riegel und Türen
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 und sprach: “Bis hierher sollst du kommen und nicht weiter; hier sollen sich legen deine stolzen Wellen!”?
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Hast du bei deiner Zeit dem Morgen geboten und der Morgenröte ihren Ort gezeigt,
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 daß sie die Ecken der Erde fasse und die Gottlosen herausgeschüttelt werden?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 Sie wandelt sich wie Ton unter dem Siegel, und alles steht da wie im Kleide.
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 Und den Gottlosen wird ihr Licht genommen, und der Arm der Hoffärtigen wird zerbrochen.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Bist du in den Grund des Meeres gekommen und in den Fußtapfen der Tiefe gewandelt?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Haben sich dir des Todes Tore je aufgetan, oder hast du gesehen die Tore der Finsternis?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Hast du vernommen wie breit die Erde sei? Sage an, weißt du solches alles!
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Welches ist der Weg, da das Licht wohnt, und welches ist der Finsternis Stätte,
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 daß du mögest ergründen seine Grenze und merken den Pfad zu seinem Hause?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Du weißt es ja; denn zu der Zeit wurdest du geboren, und deiner Tage sind viel.
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Bist du gewesen, da der Schnee her kommt, oder hast du gesehen, wo der Hagel her kommt,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 die ich habe aufbehalten bis auf die Zeit der Trübsal und auf den Tag des Streites und Krieges?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Durch welchen Weg teilt sich das Licht und fährt der Ostwind hin über die Erde?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Wer hat dem Platzregen seinen Lauf ausgeteilt und den Weg dem Blitz und dem Donner
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 und läßt regnen aufs Land da niemand ist, in der Wüste, da kein Mensch ist,
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 daß er füllt die Einöde und Wildnis und macht das Gras wächst?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Wer ist des Regens Vater? Wer hat die Tropfen des Taues gezeugt?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Aus wes Leib ist das Eis gegangen, und wer hat den Reif unter dem Himmel gezeugt,
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 daß das Wasser verborgen wird wie unter Steinen und die Tiefe oben gefriert?
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Kannst du die Bande der sieben Sterne zusammenbinden oder das Band des Orion auflösen?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Kannst du den Morgenstern hervorbringen zu seiner Zeit oder den Bären am Himmel samt seinen Jungen heraufführen?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Weißt du des Himmels Ordnungen, oder bestimmst du seine Herrschaft über die Erde?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Kannst du deine Stimme zu der Wolke erheben, daß dich die Menge des Wassers bedecke?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Kannst du die Blitze auslassen, daß sie hinfahren und sprechen zu dir: Hier sind wir?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Wer gibt die Weisheit in das Verborgene? Wer gibt verständige Gedanken?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Wer ist so weise, der die Wolken zählen könnte? Wer kann die Wasserschläuche am Himmel ausschütten,
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 wenn der Staub begossen wird, daß er zuhauf läuft und die Schollen aneinander kleben?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Kannst du der Löwin ihren Raub zu jagen geben und die jungen Löwen sättigen,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 wenn sie sich legen in ihre Stätten und ruhen in der Höhle, da sie lauern?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Wer bereitet den Raben die Speise, wenn seine Jungen zu Gott rufen und fliegen irre, weil sie nicht zu essen haben?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?

< Job 38 >