< Job 34 >

1 Und es hob an Elihu und sprach:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Hört, ihr Weisen, meine Rede, und ihr Verständigen, merkt auf mich!
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Denn das Ohr prüft die Rede, und der Mund schmeckt die Speise.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Laßt uns ein Urteil finden, daß wir erkennen unter uns, was gut sei.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Denn Hiob hat gesagt: “Ich bin gerecht, und Gott weigert mir mein Recht;
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 ich muß lügen, ob ich wohl recht habe, und bin gequält von meinen Pfeilen, ob ich wohl nichts verschuldet habe.”
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Wer ist ein solcher Hiob, der da Spötterei trinkt wie Wasser
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 und auf dem Wege geht mit den Übeltätern und wandelt mit gottlosen Leuten?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Denn er hat gesagt: “Wenn jemand schon fromm ist, so gilt er doch nichts bei Gott.”
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Darum hört mir zu, ihr weisen Leute: Es sei ferne, daß Gott sollte gottlos handeln und der Allmächtige ungerecht;
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 sondern er vergilt dem Menschen, darnach er verdient hat, und trifft einen jeglichen nach seinem Tun.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Ohne zweifel, Gott verdammt niemand mit Unrecht, und der Allmächtige beugt das Recht nicht.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Wer hat, was auf Erden ist, verordnet, und wer hat den ganzen Erdboden gesetzt?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 So er nun an sich dächte, seinen Geist und Odem an sich zöge,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 so würde alles Fleisch miteinander vergehen, und der Mensch würde wieder zu Staub werden.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Hast du nun Verstand, so höre das und merke auf die Stimme meiner Reden.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Kann auch, der das Recht haßt regieren? Oder willst du den, der gerecht und mächtig ist, verdammen?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Sollte einer zum König sagen: “Du heilloser Mann!” und zu den Fürsten: “Ihr Gottlosen!”?
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Und er sieht nicht an die Person der Fürsten und kennt den Herrlichen nicht mehr als den Armen; denn sie sind alle seiner Hände Werk.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Plötzlich müssen die Leute sterben und zu Mitternacht erschrecken und vergehen; die Mächtigen werden weggenommen nicht durch Menschenhand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Denn seine Augen sehen auf eines jeglichen Wege, und er schaut alle ihre Gänge.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Es ist keine Finsternis noch Dunkel, daß sich da möchten verbergen die Übeltäter.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Denn er darf auf den Menschen nicht erst lange achten, daß er vor Gott ins Gericht komme.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Er bringt die Stolzen um, ohne erst zu forschen, und stellt andere an ihre Statt:
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 darum daß er kennt ihre Werke und kehrt sie um des Nachts, daß sie zerschlagen werden.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Er straft sie ab wie die Gottlosen an einem Ort, da man es sieht:
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 darum daß sie von ihm weggewichen sind und verstanden seiner Wege keinen,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 daß das Schreien der Armen mußte vor ihn kommen und er das Schreien der Elenden hörte.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Wenn er Frieden gibt, wer will verdammen? und wenn er das Antlitz verbirgt, wer will ihn schauen unter den Völkern und Leuten allzumal?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Denn er läßt nicht über sie regieren einen Heuchler, das Volk zu drängen.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Denn zu Gott muß man sagen: “Ich habe gebüßt, ich will nicht übel tun.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Habe ich's nicht getroffen, so lehre du mich's besser; habe ich Unrecht gehandelt, ich will's nicht mehr tun.”
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Soll er nach deinem Sinn vergelten? Denn du verwirfst alles; du hast zu wählen, und nicht ich. Weißt du nun was, so sage an.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Verständige Leute werden zu mir sagen und ein weiser Mann, der mir zuhört:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 “Hiob redet mit Unverstand, und seine Worte sind nicht klug.”
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 O, daß Hiob versucht würde bis ans Ende! darum daß er sich zu ungerechten Leuten kehrt.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Denn er hat über seine Sünde noch gelästert; er treibt Spott unter uns und macht seiner Reden viel wider Gott.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >