< Job 33 >
1 Höre doch, Hiob, meine Rede und merke auf alle meine Worte!
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Siehe, ich tue meinen Mund auf, und meine Zunge redet in meinem Munde.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Mein Herz soll recht reden, und meine Lippen sollen den reinen Verstand sagen.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Der Geist Gottes hat mich gemacht, und der Odem des Allmächtigen hat mir das Leben gegeben.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Kannst du, so antworte mir; rüste dich gegen mich und stelle dich.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Siehe, ich bin Gottes ebensowohl als du, und aus Lehm bin ich auch gemacht.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Siehe, du darfst vor mir nicht erschrecken, und meine Hand soll dir nicht zu schwer sein.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Du hast geredet vor meinen Ohren; die Stimme deiner Reden mußte ich hören:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 “Ich bin rein, ohne Missetat, unschuldig und habe keine Sünde;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 siehe, er hat eine Sache gegen mich gefunden, er achtet mich für einen Feind;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 er hat meinen Fuß in den Stock gelegt und hat acht auf alle meine Wege.”
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Siehe, darin hast du nicht recht, muß ich dir antworten; denn Gott ist mehr als ein Mensch.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Warum willst du mit ihm zanken, daß er dir nicht Rechenschaft gibt alles seines Tuns?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Denn in einer Weise redet Gott und wieder in einer anderen, nur achtet man's nicht.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Im Traum, im Nachtgesicht, wenn der Schlaf auf die Leute fällt, wenn sie schlafen auf dem Bette,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 da öffnet er das Ohr der Leute und schreckt sie und züchtigt sie,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 daß er den Menschen von seinem Vornehmen wende und behüte ihn vor Hoffart
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 und verschone seine Seele vor dem Verderben und sein Leben, daß es nicht ins Schwert falle.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Auch straft er ihn mit Schmerzen auf seinem Bette und alle seinen Gebeine heftig
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 und richtet ihm sein Leben so zu, daß ihm vor seiner Speise ekelt, und seine Seele, daß sie nicht Lust zu essen hat.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Sein Fleisch verschwindet, daß man's nimmer sehen kann; und seine Gebeine werden zerschlagen, daß man sie nicht gerne ansieht,
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 daß seine Seele naht zum Verderben und sein Leben zu den Toten.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 So dann für ihn ein Engel als Mittler eintritt, einer aus tausend, zu verkündigen dem Menschen, wie er solle recht tun,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 so wird er ihm gnädig sein und sagen: “Erlöse ihn, daß er nicht hinunterfahre ins Verderben; denn ich habe eine Versöhnung gefunden.”
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Sein Fleisch wird wieder grünen wie in der Jugend, und er wird wieder jung werden.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Er wird Gott bitten; der wird ihm Gnade erzeigen und wird ihn sein Antlitz sehen lassen mit Freuden und wird dem Menschen nach seiner Gerechtigkeit vergelten.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Er wird vor den Leuten bekennen und sagen: “Ich hatte gesündigt und das Recht verkehrt; aber es ist mir nicht vergolten worden.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Er hat meine Seele erlöst, daß sie nicht führe ins Verderben, sondern mein Leben das Licht sähe.”
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Siehe, das alles tut Gott zwei-oder dreimal mit einem jeglichen,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 daß er seine Seele zurückhole aus dem Verderben und erleuchte ihn mit dem Licht der Lebendigen.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Merke auf, Hiob, und höre mir zu und schweige, daß ich rede!
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Hast du aber was zu sagen, so antworte mir; Sage an! ich wollte dich gerne rechtfertigen.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Hast du aber nichts, so höre mir zu und schweige; ich will dich die Weisheit lehren.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”