< Job 3 >
1 Darnach tat Hiob seinen Mund auf und verfluchte seinen Tag.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
3 Der Tag müsse verloren sein, darin ich geboren bin, und die Nacht, welche sprach: Es ist ein Männlein empfangen!
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Derselbe Tag müsse finster sein, und Gott von obenherab müsse nicht nach ihm fragen; kein Glanz müsse über ihn scheinen!
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Finsternis und Dunkel müssen ihn überwältigen, und dicke Wolken müssen über ihm bleiben, und der Dampf am Tage mache ihn gräßlich!
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 Die Nacht müsse Dunkel einnehmen; sie müsse sich nicht unter den Tagen des Jahres freuen noch in die Zahl der Monden kommen!
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 Siehe, die Nacht müsse einsam sein und kein Jauchzen darin sein!
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Es müssen sie verfluchen die Verflucher des Tages und die da bereit sind, zu erregen den Leviathan!
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Ihre Sterne müssen finster sein in ihrer Dämmerung; sie hoffe aufs Licht, und es komme nicht, und müsse nicht sehen die Wimpern der Morgenröte,
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 darum daß sie nicht verschlossen hat die Tür des Leibes meiner Mutter und nicht verborgen das Unglück vor meinen Augen!
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 Warum bin ich nicht gestorben von Mutterleib an? Warum bin ich nicht verschieden, da ich aus dem Leibe kam?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 Warum hat man mich auf den Schoß gesetzt? Warum bin ich mit Brüsten gesäugt?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 So läge ich doch nun und wäre still, schliefe und hätte Ruhe
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 mit den Königen und Ratsherren auf Erden, die das Wüste bauen,
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 oder mit den Fürsten, die Gold haben und deren Häuser voll Silber sind.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 Oder wie eine unzeitige Geburt, die man verborgen hat, wäre ich gar nicht, wie Kinder, die das Licht nie gesehen haben.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 Daselbst müssen doch aufhören die Gottlosen mit Toben; daselbst ruhen doch, die viel Mühe gehabt haben.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Da haben doch miteinander Frieden die Gefangenen und hören nicht die Stimme des Drängers.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Da sind beide, klein und groß, und der Knecht ist frei von seinem Herrn.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 Warum ist das Licht gegeben dem Mühseligen und das Leben den betrübten Herzen
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 (die des Todes warten, und er kommt nicht, und grüben ihn wohl aus dem Verborgenen,
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 die sich sehr freuten und fröhlich wären, wenn sie ein Grab bekämen),
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 dem Manne, dessen Weg verborgen ist und vor ihm von Gott verzäunt ward?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 Denn wenn ich essen soll, muß ich seufzen, und mein Heulen fährt heraus wie Wasser.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Denn was ich gefürchtet habe ist über mich gekommen, und was ich sorgte, hat mich getroffen.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 War ich nicht glückselig? War ich nicht fein stille? Hatte ich nicht gute Ruhe? Und es kommt solche Unruhe!
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”