< Job 28 >

1 Es hat das Silber seine Gänge, und das Gold, das man läutert seinen Ort.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Eisen bringt man aus der Erde, und aus den Steinen schmelzt man Erz.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 Man macht der Finsternis ein Ende und findet zuletzt das Gestein tief verborgen.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 Man bricht einen Schacht von da aus, wo man wohnt; darin hangen und schweben sie als die Vergessenen, da kein Fuß hin tritt, fern von den Menschen.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 Man zerwühlt unten die Erde wie mit Feuer, darauf doch oben die Speise wächst.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Man findet Saphir an etlichen Orten, und Erdenklöße, da Gold ist.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 Den Steig kein Adler erkannt hat und kein Geiersauge gesehen;
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 es hat das stolze Wild nicht darauf getreten und ist kein Löwe darauf gegangen.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 Auch legt man die Hand an die Felsen und gräbt die Berge um.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 Man reißt Bäche aus den Felsen; und alles, was köstlich ist, sieht das Auge.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 Man wehrt dem Strome des Wassers und bringt, das darinnen verborgen ist, ans Licht.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 Wo will man aber die Weisheit finden? und wo ist die Stätte des Verstandes?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 Niemand weiß, wo sie liegt, und sie wird nicht gefunden im Lande der Lebendigen.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 Die Tiefe spricht: “Sie ist in mir nicht”; und das Meer spricht: “Sie ist nicht bei mir”.
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Man kann nicht Gold um sie geben noch Silber darwägen, sie zu bezahlen.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 Es gilt ihr nicht gleich ophirisch Gold oder köstlicher Onyx und Saphir.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Gold und Glas kann man ihr nicht vergleichen noch um sie golden Kleinod wechseln.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 Korallen und Kristall achtet man gegen sie nicht. Die Weisheit ist höher zu wägen denn Perlen.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 Topaz aus dem Mohrenland wird ihr nicht gleich geschätzt, und das reinste Gold gilt ihr nicht gleich.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 Woher kommt denn die Weisheit? und wo ist die Stätte des Verstandes?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 Sie ist verhohlen vor den Augen aller Lebendigen, auch den Vögeln unter dem Himmel.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Der Abgrund und der Tod sprechen: “Wir haben mit unsern Ohren ihr Gerücht gehört.”
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 Gott weiß den Weg dazu und kennt ihre Stätte.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 Denn er sieht die Enden der Erde und schaut alles, was unter dem Himmel ist.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Da er dem Winde sein Gewicht machte und setzte dem Wasser sein gewisses Maß;
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 da er dem Regen ein Ziel machte und dem Blitz und Donner den Weg:
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 da sah er sie und verkündigte sie, bereitete sie und ergründete sie
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 und sprach zu den Menschen: Siehe, die Furcht des Herrn, das ist Weisheit; und meiden das Böse, das ist Verstand.
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”

< Job 28 >