< Job 26 >

1 Hiob antwortete und sprach:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Wie stehest du dem bei, der keine Kraft hat, hilfst dem, der keine Stärke in den Armen hat!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Wie gibst du Rat dem, der keine Weisheit hat, und tust kund Verstandes die Fülle!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Zu wem redest du? und wes Odem geht von dir aus?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Die Toten ängsten sich tief unter den Wassern und denen, die darin wohnen.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Das Grab ist aufgedeckt vor ihm, und der Abgrund hat keine Decke. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 Er breitet aus die Mitternacht über das Leere und hängt die Erde an nichts.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Er faßt das Wasser zusammen in seine Wolken, und die Wolken zerreißen darunter nicht.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Er verhüllt seinen Stuhl und breitet seine Wolken davor.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Er hat um das Wasser ein Ziel gesetzt, bis wo Licht und Finsternis sich scheiden.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Die Säulen des Himmels zittern und entsetzen sich vor seinem Schelten.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Von seiner Kraft wird das Meer plötzlich ungestüm, und durch seinen Verstand zerschmettert er Rahab.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Am Himmel wird's schön durch seinen Wind, und seine Hand durchbohrt die flüchtige Schlange.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Siehe, also geht sein Tun, und nur ein geringes Wörtlein davon haben wir vernommen. Wer will aber den Donner seiner Macht verstehen?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Job 26 >