< Job 21 >

1 Hiob antwortete und sprach:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hört doch meiner Rede zu und laßt mir das anstatt eurer Tröstungen sein!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Vertragt mich, daß ich auch rede, und spottet darnach mein!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Handle ich denn mit einem Menschen? oder warum sollte ich ungeduldig sein?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Kehrt euch her zu mir; ihr werdet erstarren und die Hand auf den Mund legen müssen.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Wenn ich daran denke, so erschrecke ich, und Zittern kommt mein Fleisch an.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Warum leben denn die Gottlosen, werden alt und nehmen zu an Gütern?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Ihr Same ist sicher um sie her, und ihre Nachkömmlinge sind bei ihnen.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Ihr Haus hat Frieden vor der Furcht, und Gottes Rute ist nicht über ihnen.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Seinen Stier läßt man zu, und es mißrät ihm nicht; seine Kuh kalbt und ist nicht unfruchtbar.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Ihre jungen Kinder lassen sie ausgehen wie eine Herde, und ihre Knaben hüpfen.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Sie jauchzen mit Pauken und Harfen und sind fröhlich mit Flöten.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Sie werden alt bei guten Tagen und erschrecken kaum einen Augenblick vor dem Tode, (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 die doch sagen zu Gott: “Hebe dich von uns, wir wollen von deinen Wegen nicht wissen!
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Wer ist der Allmächtige, daß wir ihm dienen sollten? oder was sind wir gebessert, so wir ihn anrufen?”
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 “Aber siehe, ihr Glück steht nicht in ihren Händen; darum soll der Gottlosen Sinn ferne von mir sein.”
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Wie oft geschieht's denn, daß die Leuchte der Gottlosen verlischt und ihr Unglück über sie kommt? daß er Herzeleid über sie austeilt in seinem Zorn?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 daß sie werden wie Stoppeln vor dem Winde und wie Spreu, die der Sturmwind wegführt?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 “Gott spart desselben Unglück auf seine Kinder”. Er vergelte es ihm selbst, daß er's innewerde.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Seine Augen mögen sein Verderben sehen, und vom Grimm des Allmächtigen möge er trinken.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Denn was ist ihm gelegen an seinem Hause nach ihm, wenn die Zahl seiner Monden ihm zugeteilt ist?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Wer will Gott lehren, der auch die Hohen richtet?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Dieser stirbt frisch und gesund in allem Reichtum und voller Genüge,
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 sein Melkfaß ist voll Milch, und seine Gebeine werden gemästet mit Mark;
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 jener aber stirbt mit betrübter Seele und hat nie mit Freuden gegessen;
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 und liegen gleich miteinander in der Erde, und Würmer decken sie zu.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Siehe, ich kenne eure Gedanken wohl und euer frevles Vornehmen gegen mich.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Denn ihr sprecht: “Wo ist das Haus des Fürsten? und wo ist die Hütte, da die Gottlosen wohnten?”
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Habt ihr denn die Wanderer nicht befragt und nicht gemerkt ihre Zeugnisse?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Denn der Böse wird erhalten am Tage des Verderbens, und am Tage des Grimms bleibt er.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Wer will ihm ins Angesicht sagen, was er verdient? wer will ihm vergelten, was er tut?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Und er wird zu Grabe geleitet und hält Wache auf seinem Hügel.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Süß sind ihm die Schollen des Tales, und alle Menschen ziehen ihm nach; und derer, die ihm vorangegangen sind, ist keine Zahl.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Wie tröstet ihr mich so vergeblich, und eure Antworten finden sich unrecht!
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >