< 1 Mose 5 >

1 Dies ist das Buch von des Menschen Geschlecht. Da Gott den Menschen schuf, machte er ihn nach dem Bilde Gottes;
Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
2 und schuf sie einen Mann und ein Weib und segnete sie und hieß ihren Namen Mensch zur Zeit, da sie geschaffen wurden.
Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
3 Und Adam war hundertunddreißig Jahre alt und zeugte einen Sohn, der seinem Bild ähnlich war und hieß ihn Seth
Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
4 und lebte darnach achthundert Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
5 daß sein ganzes Alter ward neunhundertunddreißig Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
6 Seth war hundertundfünf Jahre alt und zeugte Enos
Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
7 und lebte darnach achthundertundsieben Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
8 daß sein ganzes Alter ward neunhundertundzwölf Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
9 Enos war neunzig Jahre alt und zeugte Kenan
Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
10 und lebte darnach achthundertundfünzig Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
11 daß sein ganzes Alter ward neunhundertundfünf Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
12 Kenan war siebzig Jahre alt und zeugte Mahalaleel
Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
13 und lebte darnach achthundertundvierzig Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
14 daß sein ganzes Alter ward neunhundertundzehn Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
15 Mahalaleel war fünfundsechzig Jahre und zeugte Jared
Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
16 und lebte darnach achthundertunddreißig Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
17 daß sein ganzes Alter ward achthundert und fünfundneunzig Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
18 Jared war hundertzweiundsechzig Jahre alt und zeugte Henoch
Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
19 und er lebte darnach achthundert Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 daß sein ganzes Alter ward neunhundert und zweiundsechzig Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
21 Henoch war fünfundsechzig Jahre alt und zeugte Methusalah.
Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
22 Und nachdem er Methusalah gezeugt hatte, blieb er in einem göttlichen Leben dreihundert Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
23 daß sein ganzes Alter ward dreihundertfünfundsechzig Jahre.
Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
24 Und dieweil er ein göttliches Leben führte, nahm ihn Gott hinweg, und er ward nicht mehr gesehen.
Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
25 Methusalah war hundertsiebenundachtzig Jahre alt und zeugte Lamech
Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
26 und lebte darnach siebenhundert und zweiundachtzig Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
27 daß sein ganzes Alter ward neunhundert und neunundsechzig Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
28 Lamech war hundertzweiundachtzig Jahre alt und zeugte einen Sohn
Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
29 und hieß ihn Noah und sprach: Der wird uns trösten in unsrer Mühe und Arbeit auf der Erde, die der HERR verflucht hat.
Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
30 Darnach lebte er fünfhundert und fünfundneunzig Jahre und zeugte Söhne und Töchter;
Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
31 daß sein ganzes Alter ward siebenhundert siebenundsiebzig Jahre, und starb.
Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
32 Noah war fünfhundert Jahre alt und zeugte Sem, Ham und Japheth.
Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.

< 1 Mose 5 >