< 1 Chronik 24 >

1 Aber dies waren die Ordnungen der Kinder Aaron. Die Kinder Aarons waren: Nadab, Abihu, Eleasar und Ithamar.
Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
2 Aber Nadab und Abihu starben vor ihrem Vater und hatten keine Kinder. Und Eleasar und Ithamar wurden Priester.
Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
3 Und es ordneten sie David und Zadok aus den Kinder Eleasars und Ahimelech aus den Kindern Ithamars nach ihrer Zahl und ihrem Amt.
Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
4 Und wurden der Kinder Eleasars mehr gefunden an Häuptern der Männer denn der Kinder Ithamars. Und er ordnete sie also: sechzehn aus den Kindern Eleasars zu Obersten ihrer Vaterhäuser und acht aus den Kindern Ithamars nach ihren Vaterhäusern.
Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
5 Er ordnete sie aber durchs Los, darum daß beide aus Eleasars und Ithamars Kindern Oberste waren im Heiligtum und Oberste vor Gott.
Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
6 Und der Schreiber Semaja, der Sohn Nathanaels, aus den Leviten, schrieb sie auf vor dem König und vor den Obersten und vor Zadok, dem Priester, und vor Ahimelech, dem Sohn Abjathars, und vor den Obersten der Vaterhäuser unter den Priestern und Leviten, nämlich je ein Vaterhaus für Eleasar und das andere für Ithamar.
Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
7 Das erste Los fiel auf Jojarib, das zweite auf Jedaja,
Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
8 das dritte auf Harim, das vierte auf Seorim,
na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
9 das fünfte auf Malchia, das sechste auf Mijamin,
na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
10 das siebente auf Hakkoz, das achte auf Abia,
na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
11 das neunte auf Jesua, das zehnte auf Sechanja,
na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
12 das elfte auf Eljasib, das zwölfte auf Jakim,
na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
13 das dreizehnte auf Huppa, das vierzehnte auf Jesebeab,
na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
14 das fünfzehnte auf Bilga, das sechzehnte auf Immer,
na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
15 das siebzehnte auf Hefir, das achtzehnte auf Hapizzez,
na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
16 das neunzehnte auf Pethaja, das zwanzigste auf Jeheskel,
na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
17 das einundzwanzigste auf Jachin, das zweiundzwanzigste auf Gamul,
na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
18 das dreiundzwanzigste auf Delaja, das vierundzwanzigste auf Maasja.
na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
19 Das ist die Ordnung nach ihrem Amt, zu gehen in das Haus des HERRN nach ihrer Weise unter ihrem Vater Aaron, wie ihm der HERR, der Gott Israels, geboten hat.
Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
20 Aber unter den andern Kindern Levi war unter den Kindern Amrams Subael. Unter den Kindern Subaels war Jehdeja.
Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
21 Unter den Kindern Rehabjas war der erste: Jissia.
Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
22 Aber unter den Jizharitern war Selomoth. Unter den Kindern Selomoths war Jahath.
Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
23 Die Kinder Hebrons waren: Jeria, der erste; Amarja, der zweite; Jahasiel, der dritte; Jakmeam, der vierte.
’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
24 Die Kinder Usiels waren: Micha. Unter den Kindern Michas war Samir.
Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
25 Der Bruder Michas war: Jissia. Unter den Kindern Jissias war Sacharja.
Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
26 Die Kinder Meraris waren: Maheli und Musi, die Kinder Jaesias, seines Sohnes.
’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
27 Die Kinder Meraris von Jaesia, seinem Sohn, waren: Soham, Sakkur und Ibri.
’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
28 Maheli aber hatte Eleasar, der hatte keine Söhne.
Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
29 Von Kis: unter den Kindern des Kis war: Jerahmeel.
Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
30 Die Kinder Musis waren: Maheli, Eder und Jeremoth. Das sind die Kinder der Leviten nach ihren Vaterhäusern.
Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
31 Und man warf für sie auch das Los neben ihren Brüdern, den Kindern Aaron, vor dem König David und Zadok und Ahimelech und vor den Obersten der Vaterhäuser unter den Priestern und Leviten, für den jüngsten Bruder ebensowohl als für den Obersten in den Vaterhäusern.
Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.

< 1 Chronik 24 >