< Psalm 38 >

1 Ein Psalm Davids zum Gedächtnis. HERR, strafe mich nicht in deinem Zorn und züchtige mich nicht in deinem Grimm!
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Denn deine Pfeile stecken in mir, und deine Hand drücket mich.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 Es ist nichts Gesundes an meinem Leibe vor deinem Dräuen, und ist kein Friede in meinen Gebeinen vor meiner Sünde.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 Denn meine Sünden gehen über mein Haupt, wie eine schwere Last sind sie mir zu schwer worden.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 Meine Wunden stinken und eitern vor meiner Torheit.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 Ich gehe krumm und sehr gebückt; den ganzen Tag gehe ich traurig.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 Denn meine Lenden verdorren ganz, und ist nichts Gesundes an meinem Leibe.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 Es ist mit mir gar anders und bin sehr zerstoßen. Ich heule vor Unruhe meines Herzens.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 HERR, vor dir ist alle meine Begierde und mein Seufzen ist dir nicht verborgen.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 Mein Herz bebet, meine Kraft hat mich verlassen, und das Licht meiner Augen ist nicht bei mir.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 Meine Lieben und Freunde stehen gegen mich und scheuen meine Plage, und meine Nächsten treten ferne.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 Und die mir nach der Seele stehen, stellen mir; und die mir übel wollen, reden, wie sie Schaden tun wollen, und gehen mit eitel Listen um.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 Ich aber muß sein wie ein Tauber und nicht hören, und wie ein Stummer, der seinen Mund nicht auftut.
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 Und muß sein wie einer, der nicht höret und der keine Widerrede in seinem Munde hat.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 Aber ich harre, HERR, auf dich; du, HERR, mein Gott, wirst erhören.
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 Denn ich denke, daß sie ja sich nicht über mich freuen. Wenn mein Fuß wankete; würden sie sich hoch rühmen wider mich.
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 Denn ich bin zu Leiden gemacht, und mein Schmerz ist immer vor mir.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 Denn ich zeige meine Missetat an und sorge für meine Sünde.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 Aber meine Feinde leben und sind mächtig; die mich unbillig hassen, sind groß.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 Und die mir Arges tun um Gutes, setzen sich wider mich, darum daß ich ob dem Guten halte.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Verlaß mich nicht, HERR, mein Gott; sei nicht ferne von mir!
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.

< Psalm 38 >