< Sprueche 5 >

1 Mein Kind, merke auf meine Weisheit; neige dein Ohr zu meiner Lehre,
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2 daß du behaltest guten Rat und dein Mund wisse Unterschied zu haben.
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3 Denn die Lippen der Hure sind süß wie Honigseim, und ihre Kehle ist glätter denn Öl,
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4 aber hernach bitter wie Wermut und scharf wie ein zweischneidig Schwert.
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5 Ihre Füße laufen zum Tod hinunter, ihre Gänge erlangen die Hölle. (Sheol h7585)
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
6 Sie gehet nicht stracks auf dem Wege des Lebens; unstet sind ihre Tritte, daß sie nicht weiß, wo sie gehet.
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7 So gehorchet mir nun, meine Kinder, und weichet nicht von der Rede meines Mundes!
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8 Laß deine Wege ferne von ihr sein und nahe nicht zur Tür ihres Hauses,
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9 daß du nicht den Fremden gebest deine Ehre und deine Jahre dem Grausamen,
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10 daß sich nicht Fremde von deinem Vermögen sättigen, und deine Arbeit nicht sei in eines andern Haus,
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11 und müssest hernach seufzen, wenn du dein Leib und Gut verzehret hast,
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12 und sprechen: Ach, wie habe ich die Zucht gehasset, und mein Herz die Strafe verschmähet,
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13 und habe nicht gehorchet der Stimme meiner Lehrer und mein Ohr nicht geneigt zu denen, die mich lehreten!
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14 Ich bin schier in all Unglück kommen vor allen Leuten und allem Volk.
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
15 Trinke Wasser aus deiner Grube und Flüsse aus deinem Brunnen.
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16 Laß deine Brunnen herausfließen und die Wasserbäche auf die Gassen.
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17 Habe du aber sie alleine und kein Fremder mit dir.
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18 Dein Born sei gesegnet, und freue dich des Weibes deiner Jugend!
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19 Sie ist lieblich wie eine Hindin und holdselig wie ein Reh. Laß dich ihre Liebe allezeit sättigen, und ergötze dich allewege in ihrer Liebe.
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20 Mein Kind, warum willst du dich an der Fremden ergötzen und herzest dich mit einer andern?
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21 Denn jedermanns Wege sind stracks vor dem HERRN, und er misset gleich alle ihre Gänge.
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22 Die Missetat des Gottlosen wird ihn fahen, und er wird mit dem Strick seiner Sünde gehalten werden.
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23 Er wird sterben, daß er sich nicht will ziehen lassen, und um seiner großen Torheit willen wird's ihm nicht wohlgehen.
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.

< Sprueche 5 >