< Psalm 73 >
1 Ein Psalm Asaphs. Ja, gütig ist Gott gegen Israel, gegen die, die reines Herzens sind.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 Meine Füße aber hätten beinahe gestrauchelt; nichts fehlte, so wären meine Tritte ausgeglitten.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Denn ich ereiferte mich wegen der Übermütigen, wenn ich sah, daß es den Gottlosen so wohl ging.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 Denn sie leiden keine Schmerzen, kräftig und wohlgenährt ist ihr Leib.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Sie geraten nicht in Unglück, wie andere Leute, und werden nicht wie andere Menschen geplagt.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Darum ist Hochmut ihr Halsgeschmeide, Gewaltthat umhüllt sie als Gewand.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Aus der Verfettung stammt ihre Verschuldung, wallen die Gebilde ihres Herzens über.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Sie höhnen und reden in Bosheit, reden Bedrückung von oben herab.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 In den Himmel erheben sie ihr Maul, während sich ihre Zunge auf Erden ergeht.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Darum wendet sich sein Volk hierher, und Wasser in Fülle wird von ihnen geschlürft.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 Sie sprechen: “Wie weiß es Gott, und wie gäbe es ein Wissen darum beim Höchsten?”
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Ja, so sind die Gottlosen und in steter Ruhe häufen sie Reichtum an.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 War es denn ganz umsonst, daß ich mein Herz rein erhielt und in Unschuld meine Hände wusch -
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 und ward doch immerfort geplagt, und alle Morgen war meine Züchtigung da?
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 Wenn ich dächte: Solches will ich verkündigen, so hätte ich das Geschlecht deiner Kinder verleugnet!
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 Da sann ich nach, um es zu begreifen, aber ein Elend war es in meinen Augen,
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 bis ich in Gottes Heiligtümer eindrang, acht hatte auf ihr Ende.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Ja, auf schlüpfrigen Boden stellst du sie, stürzest sie in Trümmer.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 Wie sind sie im Nu zur Wüste geworden, haben ein Ende genommen, sind durch Schrecknisse dahin!
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Gleich einem Traume nach dem Erwachen, so verschmähst du, Herr, wenn du wach wirst, ihr Bild.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 Als mein Herz verbittert war, und es mich in den Nieren stach,
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 da war ich unvernünftig und wußte nichts, war dir gegenüber wie ein Vieh.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Aber ich bleibe stets bei dir; du hältst mich bei meiner rechten Hand.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Nach deinem Ratschlusse wirst du mich leiten und mich darnach zu Ehren annehmen.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Wen habe ich im Himmel? und außer dir begehre ich nichts auf Erden.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Wäre gleich mein Fleisch und mein Herz dahingeschwunden - Gott ist immerdar meines Herzens Fels und mein Teil!
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Denn fürwahr, die sich von dir fern halten, kommen um; du vertilgst einen jeden, der dir treulos wird.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 Mir aber ist die Nähe Gottes köstlich; in den Herrn Jahwe habe ich meine Zuflucht gesetzt, um von allen deinen Werken zu erzählen.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.