< Psalm 137 >

1 An den Strömen Babels, da saßen wir und weinten, indem wir Zions gedachten.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 An den Weiden, die dort waren, hingen wir unsere Zithern auf.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 Denn dort begehrten, die uns gefangen geführt, Lieder von uns, und unsere Peiniger Fröhlichkeit: “Singt uns eines von den Zionsliedern!”
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Wie könnten wir die Jahwe-Lieder singen auf dem Boden der Fremde!
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Wenn ich deiner vergesse, Jerusalem, so schrumpfe meine Rechte ein.
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Es klebe meine Zunge an meinem Gaumen, wenn ich deiner nicht gedenke, wenn ich nicht lasse Jerusalem meine höchste Freude sein!
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Gedenke, Jahwe, den Edomitern, den Unglückstag Jerusalems, die da riefen: “Nieder damit, nieder damit bis auf den Grund in ihr!”
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Tochter Babel, du Verwüsterin, wohl dem, der dir vergilt, was du uns angethan!
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Wohl dem, der deine zarten Kinder packt und schmettert an den Felsen.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalm 137 >