< Psalm 130 >

1 Wallfahrtslieder. Aus der Tiefe rufe ich dich, Jahwe,
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Herr, höre auf meine Stimme! Möchten deine Ohren aufmerksam sein auf mein lautes Flehn!
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Wenn du Verschuldungen im Gedächtnis bewahrtest, Jah, Herr, wer kann dann bestehen?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Vielmehr, bei dir steht die Vergebung, damit man dich fürchte.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 Ich harre auf Jahwe; meine Seele harrt auf sein Wort.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Innig warte ich auf den Herrn, sehnsüchtiger, als Wächter auf den Morgen, als Wächter auf den Morgen.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Harre, Israel, auf Jahwe! Denn bei Jahwe ist die Gnade und bei ihm Erlösung in Fülle,
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 und er wird Israel erlösen von allen seinen Verschuldungen.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalm 130 >