< Psalm 118 >
1 Danket Jahwe, denn er ist gütig; denn ewig währt seine Gnade!
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 So spreche Israel: denn ewig währt seine Gnade!
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Sprechen mögen denn die vom Hause Aarons: denn ewig währt seine Gnade!
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Sprechen mögen denn, die Jahwe fürchten: denn ewig währt seine Gnade!
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 Aus der Bedrängnis rief ich Jah; da hat mich Jah erhört und in weiten Raum gestellt.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 Jahwe ist für mich, ich fürchte mich nicht: was könnten mir Menschen thun?
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 Jahwe ist für mich, unter meinen Helfern, und ich werde meine Lust sehen an denen, die mich hassen.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 Besser ist's, bei Jahwe Zuflucht suchen, als auf Menschen vertrauen.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 Besser ist's, bei Jahwe Zuflucht suchen, als auf Fürsten vertrauen.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 Alle Heiden umringten mich - im Namen Jahwes, fürwahr, zerhaue ich sie.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 Sie umringten, ja umringten mich - im Namen Jahwes, fürwahr, zerhaue ich sie.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 Sie umringten mich wie Bienen das Wachs, brannten wie Feuer in den Dornen - im Namen Jahwes, fürwahr, zerhaue ich sie!
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 Du hast mich heftig gestoßen, damit ich fallen möchte, aber Jahwe half mir.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 Jah ist meine Stärke und mein Lobgesang, und von ihm kam mir Heil.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 Jubel- und Siegesruf erschallt in den Zelten der Frommen; die Rechte Jahwes verrichtet große Thaten.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 Die Rechte Jahwes hebt empor; die Rechte Jahwes verrichtet große Thaten.
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 Ich werde nicht sterben, sondern leben und die Werke Jahs verkündigen.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 Jah hat mich wohl gezüchtigt, aber dem Tode hat er mich nicht preisgegeben.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Thut mir auf die Thore der Gerechtigkeit: ich will durch sie eingehen, Jah zu preisen!
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 Dies ist das Thor Jahwes: Fromme gehen durch es ein.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 Ich preise dich, daß du mich erhört hast, und daß mir Heil von dir kam.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 Der Stein, den die Bauenden verworfen haben, ist zum Eckstein geworden:
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 Von seiten Jahwes ist das geschehen; wunderbar ist's in unseren Augen.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 Dies ist der Tag, den Jahwe gemacht hat: laßt uns frohlocken und fröhlich an ihm sein!
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 Ach, Jahwe, hilf doch! Ach, Jahwe, gieb doch Gelingen!
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 Gesegnet sei, wer da eingeht, im Namen Jahwes: wir segnen euch vom Tempel Jahwes aus.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 Jahwe ist Gott und er leuchtete uns. Bindet das Festopfer mit Seilen, bis an die Hörner des Altars!
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 Du bist mein Gott, und ich will dich preisen; mein Gott, ich will dich erheben!
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Danket Jahwe, denn er ist gütig, denn ewig währt seine Gnade!
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.