< Sprueche 8 >
1 Wohlan, die Weisheit ruft, und die Einsicht läßt ihre Stimme erschallen.
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Oben auf den Höhen am Wege, mitten auf den Steigen hat sie sich aufgestellt.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Neben den Thoren, wo die Stadt sich öffnet, am Eingange der Pforten ertönen ihre Rufe:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 An euch, ihr Männer, ergeht mein Ruf, und meine Stimme an die Menschenkinder.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Begreift, ihr Einfältigen, Gescheidheit, und ihr Thoren, begreift Verstand!
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Hört zu, denn was edel ist, will ich reden, und meine Lippen sollen sich öffnen zu dem, was recht ist.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Denn Wahrheit redet mein Gaumen, aber Gottlosigkeit ist meinen Lippen ein Greuel.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Rechtbeschaffen sind alle Reden meines Mundes; in ihnen ist nichts Hinterlistiges oder Falsches.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Insgesamt sind sie klar für den Verständnisvollen und einfach für die zur Erkenntnis Gelangten.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Nehmt meine Zucht lieber an als Silber und Erkenntnis lieber als auserlesenes Gold.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Denn die Weisheit ist köstlicher als Korallen, und keinerlei Kleinode kommen ihr gleich.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Ich, die Weisheit, habe Gescheidheit inne und verfüge über umsichtige Erkenntnis.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Jahwe fürchten ist Hassen des Bösen; Hoffart, Hochmut und bösen Wandel, sowie den Mund der Verkehrtheit hasse ich.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Mein ist Rat und Tüchtigkeit; ich bin Einsicht, mein ist Stärke.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Durch mich üben die Könige Königsmacht, und beschließen die Gewaltigen, was recht ist.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Durch mich üben die Herrscher Herrscheracht und die Edlen, alle Richter auf Erden.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Ich habe lieb, die mich lieb haben, und die nach mir suchen, werden mich finden.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Reichtum und Ehre sind bei mir, uraltes Gut und Gerechtigkeit.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Meine Frucht ist köstlicher als Edelmetall und Feingold, und mein Ertrag wertvoller als auserlesenes Silber.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Auf dem Pfade der Gerechtigkeit wandle ich, mitten auf den Steigen des Rechts,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 daß ich denen, die mich lieb haben, Besitztum zu eigen gebe und ihre Schatzkammern fülle.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Jahwe schuf mich als den Anfang seiner Wege, als erstes seiner Werke, vorlängst.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Von Ewigkeit her bin ich eingesetzt, zu Anbeginn, seit dem Ursprunge der Erde.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Als die Urfluten noch nicht waren, wurde ich geboren, als es noch keine Quellen gab, reich an Wasser.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Ehe die Berge eingesenkt waren, vor den Hügeln wurde ich geboren,
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 ehe er noch Land und Fluren geschaffen hatte und die Masse der Schollen des Erdkreises.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Als er den Himmel herstellte, war ich dabei, als er die Wölbung über dem Ocean festsetzte,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 als er die Wolken droben festigte, als Haltung gewannen die Quellen des Oceans,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 als er dem Meere seine Schranke setzte, daß die Wasser seinen Befehl nicht überschreiten durften, als er die Grundfesten der Erde feststellte:
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 da war ich ihm als Werkmeisterin zur Seite; da war ich ganz Entzücken Tag für Tag, spielend geschäftig vor ihm zu jeder Zeit,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 spielend auf seinem Erdenrund, und hatte mein Entzücken an den Menschenkindern.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Nun denn, ihr Söhne, gehorcht mir! Denn: wohl denen, die meine Wege einhalten!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Hört auf Zucht, daß ihr weise werdet, und schlagt sie nicht in den Wind.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Wohl dem Menschen, der mir gehorcht, so daß er Tag für Tag an meinen Thüren wacht, indem er die Pfosten meiner Thore hütet.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Denn wer mich findet, der findet Leben und erlangt Wohlgefallen von Jahwe.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Wer mich aber verfehlt, der frevelt gegen sich selbst; alle, die mich hassen, wollen den Tod.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”