< Klagelieder 5 >

1 Gedenke, Jahwe, was uns widerfahren; schau her und sieh unsere Schmach!
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Unser Erbbesitz ist Fremden zugefallen, unsere Häuser Ausländern.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Wir sind Waisen geworden, vaterlos, unsere Mütter zu Witwen.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Unser Wasser trinken wir um Geld, unser Holz bekommen wir nur gegen Zahlung.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Unsere Verfolger sitzen uns auf dem Nacken; sind wir ermattet, gönnt man uns keine Ruhe.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Ägypten reichten wir die Hand, Assur, um satt zu werden.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 unsere Väter fehlten; sie sind nicht mehr, und wir tragen ihre Verschuldungen.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Knechte herrschen über uns; niemand entreißt uns ihrer Hand.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Mit Gefahr unseres Lebens holen wir unser Brot voller Angst vor dem Schwert und der Pest.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Unsere Haut ist geschwärzt wie ein Ofen, von den Gluten des Hungers.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Frauen in Zion haben sie geschändet, Jungfrauen in den Städten Judas.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Fürsten wurden durch ihre Hand gehenkt, der Vornehmen Ansehn für nichts geachtet.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Jünglinge nahmen sie zum Mahlen, und Knaben strauchelten unter der Last von Holz.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Verschwunden sind die Greise am Thor, das Saitenspiel der Jünglinge.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Geschwunden ist unseres Herzens Freude; in Klage ist unser Reigen verwandelt.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Die Krone ist uns vom Haupte gefallen: wehe uns, daß wir gesündigt haben!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Darüber ist unser Herz siech geworden, darob unsere Augen trübe,
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 über den Zionsberg, der verwüstet ist, auf dem sich Füchse tummeln.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Du, Jahwe, thronst auf ewig, dein Stuhl steht von Geschlecht zu Geschlecht.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Warum willst du uns für immer vergessen, uns lebenslang verlassen?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Bekehre uns zu dir, Jahwe, so kehren wir um; erneuere unsere Tage, wie vor Alters!
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Oder hast du uns ganz verworfen, bist überaus auf uns erzürnt?
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Klagelieder 5 >