< Job 4 >
1 Dann antwortete Eliphas aus Theman und sprach:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Wird's dich verdrießen, wenn man ein Wort an dich wagt? Doch wer vermag der Worte Lauf zu hemmen!
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Hast du doch Viele selbst ermahnt und schlaffe Arme neu gestärkt:
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Wer strauchelte, den hielten deine Worte aufrecht, und wankenden Knieen verliehst du Kraft.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Nun, da es dich trifft, verzagst du; da dich's erfaßt, brichst du zusammen.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Ist deine Gottesfurcht nicht dein Vertrauen, und deine Hoffnung dein unsträflich Leben?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Bedenke doch, wer kam je schuldlos um, und wo wurden jemals Rechtschaffene vernichtet?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 So viel ich sah: nur, wer Unheil pflügte und Elend säte, hat es auch eingeerntet!
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Durch Gottes Odem gingen sie zu Grunde, durch seinen Zornhauch schwanden sie dahin.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 Des Löwen Brüllen und des Leuen Stimme - der jungen Löwen Zähne sind zerbrochen!
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 Der Leu kommt um, weil ihm die Beute fehlt, und zerstreuen müssen sich der Löwin Kinder.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Und zu mir drang ein verstohlenes Wort, mein Ohr vernahm davon einen flüsternden Laut -
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 bei der Gedanken Spiel infolge von Nachtgesichten, wenn tiefer Schlaf sich auf die Menschen senkt.
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Ein Beben überkam mich und ein Zittern, alle meine Gebeine geriethen in Beben.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Ein Wehen zog an mir vorüber, es sträubten sich die Haare mir am Leibe.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Dann stand - sein Aussehn konnt ich nicht erkennen - ein Gebilde vor meinen Augen; ich vernahm eine flüsternde Stimme:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 “Ist wohl ein Mensch gerecht vor Gott, vor seinem Schöpfer rein ein Mann?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 “Fürwahr, seinen Dienern traut er nicht und seinen Engeln mißt er Irrtum bei,
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 “geschweige den Lehmhüttenbewohnern, deren Sein im Staube wurzelt, die zermalmt werden wie eine Motte.
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 “Zwischen Morgen und Abend werden sie zerschmettert; ohne daß es jemand beachtet, gehn sie auf ewig zu Grunde.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 “Wird ihr Zeltstrick in ihnen zerrissen, so sterben sie dahin in Unverstand.”
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’