< Job 23 >

1 Hiob antwortete und sprach:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Auch heute empört sich meine Klage; seine Hand drückt schwer auf mein Seufzen.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 O daß ich ihn zu finden wüßte, gelangen könnte bis zu seinem Richterstuhl!
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 So wollte ich vor ihm meine Sache darlegen und meinen Mund mit Beweisen füllen.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 Ich möchte wissen, was er mir erwidern würde, und erfahren, was er zu mir sagen würde!
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 Würde er in der Fülle der Macht mit mir streiten? Nein, nur achten würde er auf mich!
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 Dann würde ein Redlicher mit ihm rechten, und für immer machte ich mich von meinem Richter frei!
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Doch - gehe ich ostwärts, so ist er nicht da, und westwärts - so gewahre ich ihn nicht.
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 Im Norden schafft er, aber ich sehe ihn nicht, biegt ab gen Süden - aber ich erblicke ihn nicht.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 Denn er weiß, welchen Wandel ich geführt - prüfte er mich, wie Gold würde ich hervorgehn.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 An seiner Spur hat fest mein Fuß gehalten, seinen Weg hab' ich verfolgt, ohne abzuweichen.
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 Von seiner Lippen Vorschrift wich ich nie, barg in meiner Brust die Worte seines Munds.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 Er aber bleibt sich gleich - wer will ihm wehren? Sein Wille begehrt's, da führt er's aus!
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 Ja, er wird zu Ende führen, was er mir bestimmt hat, und solcherlei hat er noch vieles im Sinn.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Darum erschrecke ich vor seinem Angesicht; überdenke ich's, so erbebe ich vor ihm.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 Ja, Gott hat meinen Mut gebrochen und der Allmächtige hat mich mit Schrecken erfüllt.
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 Denn nicht des Unglücks wegen fühle ich mich vernichtet, noch wegen meiner Person, die Dunkel bedeckt hat.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.

< Job 23 >