< Psalm 83 >

1 Ein Gesang, ein Lied, von Asaph. Gott, sei nicht still! Schweig nicht! Bleib nicht so ruhig, Gott!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Denn siehe, Deine Feinde sind geschäftig; das Haupt erheben Deine Hasser.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Sie halten, Deinem Volk zuwider, listig Rat, beraten gegen Deine Schutzbefohlenen.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Sie sprechen: "Auf, wir wollen sie als Volk vernichten. Nie werde mehr des Namen Israels gedacht!"
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Einmütig halten Rat und schließen gegen Dich ein Bündnis
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Edoms und Ismaels Gezelte, Moabs und die der Agarener,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, Ammon und Amalek, Philisterland und Tyrier.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Auch Assur schließt sich ihnen an; sie leihen ihren Arm den Söhnen Lots. (Sela)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Behandle sie wie Midian, wie Sisara, wie Jabin an dem Kisonsbach!
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Zu Endor wurden sie vertilgt; sie wurden Dünger für das Ackerfeld.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Tu ihren Edlen wie Oreb und Zeeb, wie Zeba und Salmunna, allen ihren Fürsten!
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Sie sprechen: "Lasset Gottes Auen uns erobern!"
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Mein Gott! Mach sie dem Wirbellaube gleich, den Stoppeln vor dem Winde!
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Wie Feuer, das den Wald verzehrt, wie Flammen, Berge sengend,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 jag ihnen nach mit Deinem Wetter! Und schreckt sie mit Deinem Sturme!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Füll an ihr Angesicht mit Schmach, auf daß sie Deinen Namen fürchten, Herr!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Sie sollen schämen sich, für immerdar verwirrt, mit Schanden untergehen!
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Dann merken sie, daß Du mit Deinem Namen heißest
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Psalm 83 >