< Psalm 78 >
1 Ein Lehrgedicht, von Asaph. - Mein Volk! Hab acht auf meine Lehre! Zu meines Mundes Reden neiget euer Ohr!
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Ich öffne meinen Mund zu einem Spruch. Ich künd Gesänge aus der Vorzeit Tagen,
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 die wir vernommen und jetzt wissen, die unsre Väter uns erzählt.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Wir, ihre Kinder, wollen über sie nicht schweigen. Wir wollen künftigem Geschlecht des Herren Ruhmestaten künden und seine Macht und Wunder, die er tat.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Zum Brauch hat er's in Jakob eingesetzt, zur heiligen Pflicht in Israel gemacht. Denn unsern Vätern hat er anbefohlen, sie ihren Kindern kundzutun,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 auf daß ein späteres Geschlecht sie kenne, die Enkel, die geboren würden, sie ihren Kindern wiederum verkünden.
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Sie sollten Gott vertrauen und nicht vergessen Gottes Taten und seine Vorschriften befolgen
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 und nicht, wie ihre Väter, werden ein widerspenstig, trotziges Geschlecht, solch ein Geschlecht von wankendem Gemüt und ungetreuem Herzen gegen Gott.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Ganz unvernünftige Söhne, voller Trug, das Leben werfen sie hinweg und wenden sich am Trübsalstage ab;
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 sie halten Gottes Bündnis nicht und wollen nicht nach seiner Lehre wandeln.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Und sie vergessen seine Werke gänzlich und seine Wunder, die er ihnen zeigt.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Vor ihren Vätern tat er Unvergleichliches, im Land Ägypten, im Gefild von Tanis.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Er spaltete das Meer und führte sie hindurch und ließ das Wasser dammgleich stehen.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Er leitete bei Tag sie mit der Wolke, die ganze Nacht mit Feuerschein,
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 und ließ die Felsen in der Wüste sprudeln und tränkte sie in Fülle wie mit Fluten.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Aus Steinen ließ er Bäche quellen, wie Ströme Wasser sprudeln.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Allein sie sündigten noch weiter gegen ihn und widersetzten sich dem Höchsten in der Wüste.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Und sie versuchten Gott in ihrem Herzen, für ihre Gelüste Speise heischend.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Sie sprachen gegen Gott und fragten: "Vermag es Gott, selbst in der Wüste einen Tisch zu decken?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Den Felsen schlug er zwar; das Wasser floß, die Bäche strömten. Vermag er aber Brot zu geben und seinem Volke Fleisch zu spenden?"
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Der Herr vernahm's und wurde zornig; ein Feuer loderte in Jakob auf; ein Zorn erhob sich gegen Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 weil sie an Gott nicht glaubten und nicht auf seine Hilfe bauten.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Doch er gebot den Wolken oben und tat des Himmels Pforten auf,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 hernieder ließ er Manna auf sie regnen, um sie zu speisen, schenkte ihnen Himmelsbrot.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Das Brot der Engel konnte jeder essen; er sandte ihnen Kost in Fülle.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Er ließ den Morgenwind am Himmel wehen; den Südwind führte er durch seine Macht herbei.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Dann ließ er Fleisch wie Staub auf sie herniederregnen, wie Meeressand Geflügel.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Er ließ es in ihr Lager fallen, um seine Wohnstatt ringsumher.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Sie aßen, wurden übersatt; was sie gewünscht, verlieh er ihnen.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Noch war nicht ihre Lust gestillt, noch war die Kost in ihrem Munde,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 als Gottes Zorn sich gegen sie erhob, die Feisten unter ihnen würgte, die junge Mannschaft Israels zu Boden streckte.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Bei all dem sündigten sie weiter und glaubten nicht an seine Wunderkräfte.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Da ließ er ihre Tage zwecklos schwinden und ihre Jahre in Enttäuschung.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Zwar fragten sie nach ihm, wenn er sie würgte, verlangten wiederum nach Gott,
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 wohl eingedenk, daß Gott ihr Hort, der höchste Gott ihr Retter sei.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Allein sie täuschten ihn mit ihrem Munde, belogen ihn mit ihrer Zunge.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Ihr Herz war unaufrichtig gegen ihn; mit seinem Bunde meinten sie's nicht ehrlich.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Doch er, erbarmungsvoll, vergab die Schuld, vertilgte nicht; oft hielt er seinen Zorn zurück und ließ nicht seinen Grimm austoben,
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 wohl eingedenk, daß sie nur Fleisch, ein Windhauch, der verschwindet ohne Wiederkehr.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Wie oft erzürnten sie ihn in der Wüste und reizten ihn im Steppenland,
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 versuchten immer wieder Gott, erbitterten die Heiligen Israels,
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 gedachten nimmer seiner Macht, des Tages, da er vor dem Feinde sie gerettet,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 wie er vor den Ägyptern seine Zeichen tat, an dem Gefild von Tanis seine Wunder:
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 In Blut verwandelte er ihre Ströme; untrinkbar ward ihr fließend Wasser.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Er sandte Ungeziefer unter sie, das sie verzehrte, und Frösche ihnen zum Verderben.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Der Raupe gab er ihre Früchte preis und ihre Arbeit der Heuschrecke.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Er schlug mit Hagel ihren Weinstock und ihren Maulbeerbaum durch Reif.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Er gab ihr Vieh dem Hagel preis, den Blitzen ihre Herden.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Er ließ die Hitze seines Zornes auf sie los, nur Grimm und Wut und Angst, von Unglücksboten eine Schar.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 So ließ er seinem Zorne freien Lauf, verschonte ihre Seele mit dem Tode nicht. Er gab der Pest ihr Leben preis,
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 und in Ägypten schlug er alle Erstgeburt, die Jugendblüte in den Zelten Chams.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Er führte, Schäflein gleich, sein Volk heraus und lenkte sie wie in der Steppe eine Herde.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Er leitete sie sicher, daß sie nichts zu fürchten hatten; das Meer bedeckte ihre Feinde.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Er brachte sie zu seinem heiligen Gebiete, zu jenem Berg, den seine Rechte sich erworben,
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 vertrieb vor ihnen weg die Heiden, verloste sie als erblichen Besitz und ließ die Stämme Israels in ihren Zelten wohnen.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Und doch versuchten sie und reizten Gott, den Höchsten, und hielten nimmer seine Satzungen.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Wie ihre Väter wichen sie und fielen ab; sie wurden wie ein schlaffer Bogen.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Sie reizten ihn zum Zorn durch ihre Höhen, zur Eifersucht durch ihre Götzenbilder.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Gott hörte dies und wurde zornig, und Israel verwarf er völlig,
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 verließ zu Silo seinen Sitz, das Zelt, in dein er unter Menschen wohnte;
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 gab seine Ehre in Gefangenschaft und seine Zier in Feindeshand
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 und gab sein Volk dem Schwerte preis, entrüstet über dies sein Eigentum.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Die jungen Männer fraß das Feuer, und seine Jungfraun durften keine Totenklage halten.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Hinfielen seine Priester durch das Schwert, und seine Witwen weinten nicht dazu.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Doch wie vom Schlaf erwachte da der Herr, gleichwie ein Held vom Weine jauchzend.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Im Rücken schlug er seine Feinde, belegte sie mit ewigem Schimpf.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Doch er verschmähte Josephs Zelt; den Stamm von Ephraim erkor er nicht.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Vielmehr erkor er Judas Stamm, den Sionsberg, der ihm so lieb.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Er baute Himmelshöhen gleich sein Heiligtum und gleich der Erde, die er ewig gründete.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Und er erkor sich David, seinen Knecht, entriß ihn seiner Herde Hürden.
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Vom Milchvieh nahm er ihn hinweg, sein Volk zu weiden in Jakob, in Israel die ewig Seinen.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Mit frommem Sinne weidete er sie und führte sie mit kluger Hand.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.