< Psalm 63 >
1 Ein Lied, von David, als er in der Wüste Juda war. Dich such ich, Gott, mein Gott; nach Dir lechzt meine Seele; nach Dir sehnt sich mein Fleisch. Wie in dem dürren, trocknen, wasserlosen Lande,
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2 so schau ich aus nach Dir, um Deine Pracht zu sehen und Deine Majestät im Heiligtum.
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3 Denn köstlicher ist Deine Huld als Leben. Dich preisen meine Lippen.
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4 So preise ich Dich lebenslang; in Deinem Namen will ich regen meine Hände.
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5 Gleichwie von Fett und Öl wird meine Seele satt; mit Jubellippen singt mein Mund,
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6 wenn ich auf meinem Lager Dein gedenke, in mitternächtiger Stunde sinne über Dich,
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7 Du möchtest Schutz mir sein, daß ich im Schatten Deiner Flügel jauchze.
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8 An Dir hängt meine Seele; ich klammere mich an Deine Rechte.
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9 Die meine Seele gerne in der Wüste wüßten, sie mögen in der Erde Tiefe fahren!
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10 Die sie dem Untergange überliefern wollen, die mögen der Schakale Beute werden!
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11 Der König aber freue sich in Gott, und wer ihm Treue schwört, der jauchze! Der Lügner Mund wird zugestopft.
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.