< Psalm 38 >
1 Ein Lied; von David, zum Erlernen. Bestraf mich nicht in Deinem Zorne, Herr! In Deinem Grimme züchtige mich nicht noch mehr!
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Denn Deine Pfeile sind gar tief in mich gedrungen, und Deine Hand liegt schwer auf mir.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 An meinem Fleische ist nichts heil ob Deinem Zorn, nichts unversehrt an meinem Leib ob meiner Sünde.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 Denn meine Sünden übersteigen mir das Haupt, sind mir zu schwer, wie eine ungeheure Last.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 Und eiternd faulen meine Wunden um meiner Torheit willen.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 Ich winde mich und krümme mich so heftig und allzeit gehe ich betrübt einher.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 In meinem Innern wühlt der Brand; an meinem Leib ist nichts Gesundes.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 Ich bin gelähmt, zermalmt und stöhne; mir klopft das Herz.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Vor Dir liegt jeder meiner Wünsche offen, Herr; mein Seufzen ist Dir nicht verborgen.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 Mir pocht das Herz und steht mir still, und meine Kraft, mein Augenlicht versagen mir den Dienst.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 Die Freunde und Gefährten treten zurück vor meiner Plage; fern stehen die Verwandten mir.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 Die auf mein Leben lauern, legen Schlingen, und die mein Unglück suchen, drohen mit Verderben und schmieden täglich Ränke.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 Und ich? Ich bin wie taub und höre nichts, bin wie ein Stummer, der den Mund nicht öffnet,
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 bin wie ein Mensch, der nichts versteht und keinen Widerspruch im Munde führt.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 Denn ich vertraue, Herr, auf Dich; Du Herr, mein Gott, wirst Rede stehen,
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 Weil ich mir sag, sie dürfen meiner nimmer spotten, und glitte aus mein Fuß, nicht über mich frohlocken.
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 Schon bin ich ja dem Falle nah, stets meiner Schwäche mir bewußt.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 Denn ich bekenne meine Schuld und gräme mich um meine Sünde.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 Doch zahlreich sind, die unverschuldet mich befeinden, und viele, die mich grundlos hassen,
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 und die mit Bösem Gutes mir vergelten, mich lästern, daß ich nach dem Guten strebe.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Verlaß mich nicht, o Herr! Mein Gott, entfern Dich nicht von mir!
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Zu meinem Schutze schnell herbei! Zu Hilfe, Herr!
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.