< Psalm 37 >
1 Von David. - Ereifere dich nicht der Bösewichte wegen! Beneide nicht die Übeltäter!
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 Sie welken schnell wie Gras, verdorren wie das grüne Kraut.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Vertrau dem Herrn! Tu Gutes! Verbleib im Land, dich redlich nährend!
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Wie ein verwöhntes Kind komm zu dem Herrn! Er gibt dir, was dein Herz sich wünscht.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Befiehl du deinen Weg dein Herrn! Auf ihn vertrau! Er wird's schon machen.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 Er bringt ans Licht, daß du gerecht, und an den Tag, daß du im Recht.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Und schweig zum Herrn und harre sein! Ereifere über den dich nicht, der sich Erfolg erzwingt, nicht über einen Mann, der Schwindel treibt!
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Gib auf den Ärger! So ereifere dich nicht, daß selbst du Böses tätest!
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 Denn ausgerottet werden Übeltäter; die auf den Herrn vertrauen, bleiben im Besitz des Landes.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Noch kurze Zeit! Dann ist der Bösewicht dahin! Du schaust nach seiner Stätte. Er ist nicht mehr.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 Die Dulder bleiben im Besitz des Landes an reichem Glücke sich erlabend.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 Dem Frommen plant zuleid der Frevler Arges und fletscht die Zähne wider ihn.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 Der Herr lacht seiner; schon sieht er seinen Tag sich nahen.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 Die Frevler zücken zwar ihr Schwert und spannen ihren Bogen, um Elende und Arme zu erlegen und hinzuwürgen, die geraden Wandels.
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Allein ihr Schwert dringt in ihr eigen Herz, und ihre Bogen splittern.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Das Wenige bekommt dem Frommen besser, als Frevlern großer Reichtum.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 Zerbrochen werden ja der Frevler Arme; die Frommen aber stützt der Herr.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 Der Herr sorgt für die Tage lauterer Menschen, und ihr Besitztum dauert immerfort.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 Sie werden nicht in böser Zeit zuschanden; sie werden satt in Hungertagen.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 Denn nur die Frevler gehn zugrunde, des Herrn Feinde gleich der Auen Pracht; sie schwinden hin wie Rauch; sie schwinden.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 Der Frevler borgt, kann's aber nicht zurückerstatten; freigebig, milde kann der Fromme sein.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 Denn die von ihm Gesegneten verbleiben im Besitz des Landes; doch die von ihm Verfluchten werden ausgerottet.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 Sind eines Mannes Schritte recht im Hinblick auf den Herrn, dann kümmert dieser sich um seinen Weg.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Und wankt er auch, so stürzt er nicht; ihn stützt der Herr mit seiner Hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Ich war ein Jüngling, ward ein Greis; doch ganz verlassen habe ich den Frommen nie gesehen, noch sein Geschlecht um Nahrung betteln.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 Stets milde, leiht es allezeit; zum Segen sät es aus.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Dem Laster gram, der Tugend hold, so bleibst du immerdar.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 Der Herr liebt ja das Recht; von seinen Frommen läßt er nicht. Sie sind für alle Zeit geschützt; der Frevler Brut wird ausgerottet.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 Den Frommen wird das Land zu eigen, sie bleiben ewiglich darin.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 Des Frommen Mund spricht Weises; nur Rechtes redet seine Zunge.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 Im Herzen trägt er seines Gottes Lehre, und seine Schritte schwanken nie.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 Der Frevler lauert auf dem Frommen, begierig, ihn zu morden.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Doch überläßt der Herr ihn nimmer seiner Hand, läßt vor Gericht ihn nicht verdammen.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Dem Herrn vertrau! Halt dich an seinen Weg! Dann gibt er dir das Land zu eigen; der Frevler Untergang erlebst du noch.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 Ich habe einen Frevler voller Trotz gesehen, so kahl gemacht wie Gras im Felde.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Man schaute um; er war nicht mehr. Ich suchte ihn; er war nicht mehr zu finden.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Merk auf die Lauteren! Schau auf die Redlichen, wie's jedem gut am Ende geht!
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 Die Missetäter aber werden all vertilgt; der Frevler Zukunft wird vernichtet.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 Der Frommen Heil dagegen kommt vom Herrn; er ist ihr Schutz zur Zeit der Not.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 Der Herr steht ihnen bei und rettet sie; er schirmt und schützt sie vor dem Bösen; denn sie vertraun auf ihn.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.