< Psalm 33 >

1 Ihr Frommen, jauchzt dem Herrn! Den Redlichen ziemt Lobgesang.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Mit Zitherklängen dankt dem Herrn! Ihm spielt auf Harfen mit zehn Saiten!
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Ihm singt ein nie gehörtes Lied! Und schlaget kräftig in die Saiten, daß es schallt!
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 Wahrhaftig ist das Wort des Herrn, und Treue ist sein ganzes Tun.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Er liebt Gerechtigkeit und Recht; des Herrn Güte ist die Erde voll.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Die Himmel sind geworden durch das Wort des Herrn, durch seines Mundes Hauch ihr ganzes Heer.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Er sammelt wie in einen Schlauch ein Meer von Wasser und legt in Speicher Ozeane.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 So fürchte alle Welt sich vor dem Herrn! Vor ihm erschauere jeder Erdbewohner!
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 Denn so er spricht, geschieht's, gebietet er's, so bleibt es aus.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 Zunichte macht der Herr der Heiden Plan; der Völker Absichten vereitelt er.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 Der Plan des Herrn ist unveränderlich, und seines Herzens Pläne gelten für und für.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Heil sei dem Heidenvolke, dessen Gott der Herr, der Nation, die er zur ewig Seinen sich erkoren!
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 Vom Himmel schaut der Herr herab und blickt auf alle Menschenkinder!
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Von seiner Wohnstatt schaut er nieder auf alle Erdbewohner.
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 Ihm, der geschaffen ihre Herzen allzumal, dem ist bekannt ihr ganzes Tun.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 Kein König siegt durch Heeresmacht; den Riesen rettet nicht die Fülle seiner Kraft.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Betrogen, wer vom Roß den Sieg erwartet; nicht Rettung bringt es ihm trotz großer Stärke.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Auf denen, so ihn fürchten, ruht des Herrn Auge, auf denen, die von seiner Güte hoffen,
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 daß er vor Pest ihr Leben rette und sie in Hungersnot erhalte.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Dem Herrn gilt unserer Seele Harren; uns ist er Schutz und Schild.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 So froh wird unser Herz durch ihn; denn wir vertrauen seinem heiligen Namen.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Herr! Deine Gnade walte über uns, so wie wir sie von Dir erhoffen!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Psalm 33 >