< Psalm 135 >
1 Alleluja! Lobpreist des Herren Namen! Lobpreist ihn ihr, des Herren Diener,
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 die ihr im Haus des Herren weilet, in unseres Gotteshauses Höfen!
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Singt Alleluja! Denn der Herr ist gut. Singt seinem Namen! Er ist liebreich,
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 hat doch der Herr sich Jakob auserkoren, zu seinem Eigentum sich Israel. -
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Ich weiß, der Herr ist so gewaltig, daß unser Herr die Götter alle überragt.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Der Herr tut, was er will, im Himmel und auf Erden, im Meer und in den Tiefen all.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Der Du heraufführst Wolken von der Erde Ende und Blitze für den Regen bildest, der Du den Wind aus seinen Kammern lässest,
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 der Du die Erstgeburt Ägyptens schlugest, vom Menschen bis zum Vieh,
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 und in Ägypten wunderbare Zeichen an Pharao und allen seinen Knechten tatest
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 und große Völker niederschlugst und starke Könige vertilgtest,
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 den Amoriterkönig Sichon, den Basankönig Og und alle Reiche Kanaans
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 und deren Land zum ewigen Besitze machtest, zum ewigen Besitze Deines Volkes Israel.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Dein Name ist auf ewig "Herr", für alle Zeiten wirst Du "Herr" genannt. -
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Der Herr schafft seinem Volke Recht, erbarmt sich seiner Diener.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Der Heiden Götzen sind von Gold und Silber, der Menschenhände Werk.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Sie haben einen Mund und reden nicht und Augen, doch sie sehen nicht.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Nicht hören sie mit ihren Ohren; kein Odem ist in ihrem Mund.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Wie sie, so sollen werden, die sie machen, und so, wer sich auf sie verläßt! -
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Lobpreis den Herrn, Haus Israel! Du Aaronshaus, Lobpreis den Herrn!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Du Levis Haus, Lobpreis den Herrn! Die ihr den Herrn fürchtet, preist den Herrn!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Gepriesen sei der Herr von Sion aus, der thronet zu Jerusalem! Alleluja!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.