< Psalm 114 >

1 Als Israel Ägypten und Jakobs Haus das fremde Volk verließ,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 da ward Juda sein Heiligtum und Israel sein Reich.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 Dies sah das Meer und floh; der Jordan ging zurück.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 Die Berge hüpften gleich den Widdern, die Hügel wie die Lämmer. -
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 Was ist dir, Meer? Du fliehst. Was, Jordan, dir? Du gehst zurück.
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Euch Bergen, daß ihr gleich den Widdern, euch Hügeln, daß ihr gleich den Lämmern hüpfet; -
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Erbebe, Erde, vor dem Herrn, vor Jakobs Gott,
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 der Fels in See und Kies in Quellgrund wandelt!
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Psalm 114 >