< Sprueche 8 >

1 Die Weisheit! Ruft sie nicht? Und Einsicht läßt sich hören
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 am Weg ganz oben auf den Höhen; an Scheidewegen tritt sie auf.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Beim Eingang in die Stadt, an ihren Toren, am Eingang zu den Pforten ruft sie aus:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 "Zu euch, ihr Männer, rede ich; ich spreche zu den Menschenkindern:
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Ihr Einfältigen, lernet Klugheit! Ihr Toren, kommet zur Vernunft!
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Hört zu! Denn ich will Rechtes reden, und meiner Rede Inhalt ist, was richtig.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Denn Redlichkeit nur spricht mein Gaumen; für meine Lippen ist Unehrlichkeit ein Greuel.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Rechtschaffen ist, was immer spricht mein Mund, nichts Hinterlistiges, nichts Falsches ist darin,
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 das Richtige für alle, die da fragen, und recht für die, die suchen nach Erkenntnis.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Nimm meine Mahnung lieber an als Silber, Erkenntnis lieber als erlesenes Gold. -
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Denn besser noch als Perlen ist die Weisheit; und Kostbarkeiten kommen ihr nicht gleich."
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 "Ich, Weisheit, hab zur Nachbarin die Klugheit; ich kann zu klugem Wissen kommen.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Die Furcht des Herrn verträgt sich nicht mit Bösem. Ich hasse Hochmut, Hoffart, schlimmen Wandel sowie verkehrtes Reden.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Mein ist der Rat, die Tüchtigkeit; Einsicht ist mein und mein die Stärke.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Durch mich regieren Könige, und Fürsten herrschen, wie es rechtens ist.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Durch mich befehlen Herrschende und all die hohen Erdenrichter.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Wer mich liebt, den liebe ich; mich finden, die mich suchen,
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Reichtum und Ehre sind bei mir, ein stattlich Gut und Wohlergehen.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Weit besser noch als Gold, als feines Gold, ist meine Frucht, und mein Ertrag ist kostbarer als auserlesen Silber.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Ich wandle auf dem Pfade der Gerechtigkeit und mitten auf des Rechtes Wegen.
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 Ich gebe denen, die mich lieben, immerdar Besitz und fülle ihre Schatzkammern."
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Mich schuf der Herr als Anfang seiner Laufbahn, als erstes seiner Werke,
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 in der Urzeit. Von Ewigkeit her bin ich eingesetzt, im Anfang seit dem Weltbeginne.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Die Ozeane waren nicht, da ward ich schon geboren, als es noch keine reichen Wasserquellen gab.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Bevor die Berge eingesenkt, da war ich vor den Hügeln schon geboren.
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Er hatte Land und Flur noch nicht gemacht, noch nicht das Element des Staubes in der Welt,
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 da war ich schon dabei, als er den Himmel hergestellt, als er die Wölbung überm Ozean festsetzte,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 als er die Wolken droben mächtig machte, und als des Ozeanes Fluten mächtig wurden,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 als er dem Meere seine Schranke setzte, daß die Gewässer sein Geheiß nicht überschritten, als er der Erde Gründe legte.
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Zur Seite war ich ihm als Schülerin und diente zur Ergötzung Tag für Tag und spielte vor ihm jede Zeit
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 und spielte auf dem Erdkreis, den ich liebte, und zur Ergötzung diente ich den Menschenkindern."
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 "Nun, meine Söhne, hört auf mich! Heil denen, die meine Wege wählen!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Auf Mahnung hört, auf daß ihr weise werdet! Schlagt sie nicht in den Wind!
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Heil sei den Menschen, die mich hören und Tag für Tag an meinen Türen wachen und meiner Tore Pfosten hüten!
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Denn wer mich findet, findet Leben, und von dem Herrn empfängt er alles Nötige.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Wer aber mich verfehlt, der frevelt gegen seine eigene Seele; ja alle, die mich hassen, lieben nur den Tod."
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Sprueche 8 >