< Sprueche 5 >

1 Mein Sohn! Merk wohl auf meine Weisheit und neige meiner Einsicht hin dein Ohr!
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2 Alsdann behältst du Einsicht, und deine Lippen wahren Klugheit.
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3 Von Honigseim triefen die Lippen eines fremden Weibes; sein Gaumen ist noch glätter selbst als Öl.
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4 Am Ende aber ist sie bitter wie der Wermut und scharf wie ein zweischneidig Schwert.
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5 Zum Tode gehn die Füße, die sie besuchen, zur Unterwelt die Schritte, die zu ihr lenken. (Sheol h7585)
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
6 Geht sie den Weg des Lebens? Irrpfade nur sind ihre Bahnen; sie weiß es nicht.
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7 Nun, meine Söhne, hört auf mich! Von meines Mundes Reden weichet nicht!
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8 Halt ferne deinen Weg von ihr! Komm nicht der Türe ihres Hauses nahe!
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9 Sonst mußt du deine Kraft mit einer Fremden, mit einer Unbarmherzigen dein Lager teilen.
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10 Und Fremde werden satt durch deine Arbeit, und deiner Mühen Preis wird einem andern Haus zuteil.
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11 Und schließlich mußt du stöhnen, wenn Leib und Fleisch dir schwinden,
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12 und mußt bekennen: "Ach, daß ich Zucht gehaßt und daß mein Herz die Warnung hat verschmäht,
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13 daß ich der Stimme meiner Lehrer nicht gehorcht und nicht mein Ohr geliehen meinen Lehrmeistern!
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14 Fast wäre ich geworden "alles Böse in der Gemeinde und Versammlung".
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
15 Aus deiner Grube Wasser trink; nur was aus deinem Brunnen quillt!
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16 Nicht sollen deine Ströme sich nach außen gießen, nicht auf die freien Plätze deine Wasserbäche!
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17 Sie sollen dir allein gehören und nicht den Fremden neben dir!
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18 Gesegnet sei dein Born! Erfreu dich an dem Weibe deiner Jugend,
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19 an dieser Hindin gar so lieb, an der Gazelle, also fein! Allzeit kann ihre Liebe dich berauschen; du kannst dich ihrem Lieben immerdar ergeben.
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20 Warum nur wolltest du, mein Sohn, dich einer anderen ergeben, umarmen einer Fremden Busen?
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21 Klar liegen vor des Herren Auge eines jeden Wege; auf alle seine Pfade hat er acht.
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22 Den Frevler nimmt gefangen seine Schuld; gebunden wird er mit den Stricken seiner Sünde.
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23 Er stirbt aus Mangel an Botmäßigkeit und durch die große Torheit, der er sich ergeben.
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.

< Sprueche 5 >